fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Ina baiwa Gwamna El-Rufai Shawara kada ya tsawaita nadin sabon sarkin Zazzau saboda kar mutane su fara zarginsa>>Hakeem Baba Ahmad

Uban kasa a jihar Kaduna, Dr. Hakeem Baba Ahmad ya baiwa gwamnan Kadunan shawarar cewa kada ya tsawaita maganar nadin sabon sarkin Zazzau.

 

Yace dalili kuwa shine Allah ne kawai me yin daidai kuma ba za’a iya farantawa kowa ba. Yace tsawaita nadin sarkin ka iya sa kutane su fara zargin Gwamnan da cewa, yana son nada nasa sarkin ne.

Dr. Hakeem ya bayar da wannan shawara ne ta shafinsa na Twitter.

A jiyane dai gwamnan ya tabbatar da karbar sunayen mutane 11 wanda daga cikine za’a dauki wanda za’a nada Sarki.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *