Ranar Alhamis, 13 ga watan Fabarairun 2020 tsohon shugaban mulkin sojin Najeriya, Janar Murtala Ramat Mohammed ke cika shekara 44 da rasuwa.
Wasu sojoji da suka yi yunkurin juyin mulki ne suka kashe tsohon shugaban Najeriyar ranar 13 ga watan Fabrairun shekarar 1976 a Lagos.
An harbe shi ne a yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa wurin aiki.
Murtala Mohammed shi ne mutum na hudu da ya zama shugaban Najeriya tun bayan samun ‘yancin kanta daga turawan mulkin mallakar Birtaniya a 1960.
Akasarin ‘yan kasar na tuna irin jajircewar da ya yi wajen yaki da rashawa da cin hanci da kawo tsari ga aikin gwamnati da son ci gaban kasa.
BBChausa.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:
A shafin twitter zaku same mu a @hutudole
A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa
Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole