Mawallafin Sahara Reporters, Omoyele Sowore ya mayar da martani kan ikirarin dan majalisar da yace sai APC ta kai shekaru 100 tana Mulkin Najeriya.
Dan majalisar Yusuf Gagdi ya bayyana hakane bayan ya sabunta rijistarsa ta jam’iyyar a jiharsa ta Filato.
Saidai Sowore ya bayyana cewa hakan ba gaskiya bane saboda jam’iyyar APC ta mutu kuma Rijistar da ake yi ba inda zata kaita, yace irin cika bakin da PDP ta yi kenan a baya.
This is what they say when their party is on a freefall! @OfficialAPCNg is dead, their current fake registration exercise is the post mortem, ask @OfficialPDPNig what happened after they bragged they’ll rule for 60yrs! Pride comes before fall #RevolutionNow