fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Kamin in sauka daga mulki sai na cika Alkawuran kawo canjin dana yiwa ‘yan Najeriya>>Shugaba Buhari

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa kamin ya sauka daga mulki sai ya cika alkawuran da yawa ‘yan Najeriya a shekarar 2015.

 

Yace har yanzu yana nan kan bakarsa na kawo canji a kasarnan.

 

Shugaban ya bayyana bangaren samar da gidaje a matsayin wani bangare da gwamnatinsa ta yi kokari sosai akai.

 

Shugaban ya bayyana hakane a wajan kaddamar da wasu rukunin gidajen gwamnatin tarayya 68 data gina a akan titin Benin zuwa Auchi a jihar Edo.

 

Ya bayyana cewa a lokacin da yake neman mulki a 2015 ya yiwa ‘yan Najeriya alkawarin canji, to wadannan gidajen da aka gina suna daya daga cikin canje-canjen da ya kawo.

Karanta wannan  Gwamnatin Tinubu ta bayar da umarnin ci gaba da aikin titin jirgin kasa daga Fatakwal zuwa Maiduguri

 

 

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *