Kotu a babban burnin Tarayya, Abuja, Kubwa ta kwace ‘ya’yan dan gidan tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar wanda shima sunansa Atiku Abubakar ta baiwa tsohuwar matarsa, Maryam Sharif.
A shekarar data gabata ne, Maryam ta kai karar tsohon mijin nata a Gudu wanda daga baya aka mayar da karar Kubwa.
Tana nemana ne kotu ta bata damar rike yaransu 3.
Mai shari’a, Bashir Dan mai sule da yake yanke Hukunci a Ranar Laraba yace wanda ake kara ya kasa kare kansa dan haka an baiwa tsohuwar matar tasa damar rike yaran 3.
Saidai wanda aks kara na da kwanaki 30 ya daukaka karan.