fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Kungiyar ISWAP ta dauki alhakin kai harin bam a Taraba yayin da adadin wadanda suka mutu ya haura shida

Mayakan jihadi da ke da alaka da kungiyar IS sun dauki alhakin harin bam din da ya tashi a wata mashaya ta shan giya a kasuwar Mashaya, unguwar Iware a karamar hukumar Ardo-Kola a jihar Taraba.

An tabbatar da mutuwar mutane shida a harin wanda ya faru ranar Talata yayin da mutane kusan 20 ke samun kulawa a asibitoci biyu.

An tura wadanda suka samu mummunan raunuka zuwa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya, FMC, a Jalingo.

A cikin wata sanarwa da ta fitar da harshen Larabci a ranar Larabar da ta gabata, kungiyar IS da ke yammacin Afirka (ISWAP) ta ce ta tayar da bam din tare da kashe kusan kiristoci 30 tare da lalata mashayar.

A cewar Channels TV, sanarwar da SITE Intelligence da ke sa ido kan ayyukan jihadi a duniya ta fassara, ta ce harin “ramuwar gayya” ne na mutuwar shugabannin kungiyar biyu, ba tare da bayar da karin bayani ba.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *