fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

‘Yar kauye ta zo birni: Wani ya gayawa Nafisa Abdullahi bayan data wallafa wadannan hotunan nata daga kasar Ingila

Tauraruwar fina-finan Hausa Nafisa Abdullahi kenan a kusa da tambarin kulub din wasan kwallon kafa na Chelsea, jiya ne dai Ali Nuhu da Ita da Ramadan Booth sukaje kallon wasan da aka buga tsakanin Chelsea din da Manchester United, wadannan kari ne akan hotunan jiyan.

Jaruman na Fina-finan Hausan dai sunje kasar Ingilane inda aka karramasu da wasu lambobin yabo wanda jaridar African Voice ta basu

Ali Nuhu ne ya musu jagora zuwa gurin karbar wadannan kyautukan da aka basu.

Bayan da aka gama bikin karramasu dinne sai suka fantsama gari dan kashe kwarkwatar idanunusu.

Bayan data wallafa wadannan hotunan nata ne a dandalinta na sada zumunta da muhawara sai wani ya mata tsiya da cewa, “‘yar kauye anzo birni”

Dukkansu muna musu fatan Alheri da kuma Allah yasa su gama abinda suke lafiya su dawo gida Najeriya lafiya.

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *