Masu garkuwa da Mutane dan neman kudin fansa sun kashe wani jami’in civib Defence da suka yi garkuwa dashi, Mr. Bulus Sanda.
Masu garkuwa da mutanen sun yi garkuwa dashine a gidansa dake Marabar Rido dake Kaduna, kamar yanda hukumar ta bayyana.
A sanarwar da NSCDC ta fitar ta bakin shugabanta na Kaduna, Babangida Abdullahi Dutsin Man ta mikawa iyalan mamacin sakon ta’aziyya tare kuma da kira ga mutane su rika bada hadin kainwajan kai rahoton duk wani lamari da basu gane ba.
Hukumar ta bayyana marigayin a matsayin haziki da ke nuna kwarewa a aikinsa.