fbpx
Thursday, December 7
Shadow

Membobin APC kadai zan marawa baya a zaben 2023 banda wa’yanda suka maka mu a kotu , cewar shugaba Buhari

Shugaban kasa Muhammdu Buhari ya bayyana cewa membobin jam’iyyarsa ta APC kadai zai marawa baya a zaben shekarar 2023.

Hadimin shugaban kasa Garba Shehu ne ya bayyana hakan a ranar laraba, inda yace har yanzu Buhari jigon jam’iyyar APC ne kuma zai tsayawa ‘yan takarar dake jam’iyyar suyi nasara.

Sai dai fa ba zai taba tsayawa wa’yanda basa jam’iyyar ba da kuma wa’yanda suka sauya sheka dama masu maka su a kotu bakidaya.

Amma yace yana maraba da duk wata jam’iyyar dake shirin mara masu baya sai dai su kam babu wanda zasu marawa baya face dan jam’iyyarsu.

Karanta wannan  Kalli Bidiyo: Yanda naman Mutane yake makalewa a takalman masu ceto a wajan Maulidi da ake zargin sojoji sun jefa Bam a Kaduna

A karshe shugaban kasar ya kara da cewa bada wata jam’iyyar adawa yake wannan maganar ba ra’ayinsa ne kawai ya fadi.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *