fbpx
Thursday, December 7
Shadow

Mutane miliyan daya muka kashe domin a samu zaman lafiya a Najeriya, cewar shugaba Buhari

Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa mutane miliyan ne suka rasa rayukansu a yakin Biafra domin a samu zaman lafiya a Najeriya.

Inda shugaban kasar yace bai kamata a sake barin irin wannan bala’in ya sake faruwa a wannan kasar ba wanda ya faru a shekarar 1967 zuwa 1970.

Shugaban kasar ya bayyana hakan ne a yau ranar talata yayin da shuwagabannin tsohuwar jam’iyyarsa ta CPC ta kai masa ziyara a fadarsa.

Inda yace ya kamata a hada kan Najeriya wuri guda domin a samu lafiya, kuma yana matukar godiya a garesu da kuma jinjina bisa goyon bayansa da suke yi.

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *