Tauraron dan wasan Real Madrid, Karim Benzema ya bayyana cewa yayi iya kokarinsa da zaisa ya lashe kyautar Ballin D’or bayan ya taimakawa Madrid ta doke Liverpool 1-0 ta lashw kofin zakarun nahiyar turai.
Benzema baici kwallo a wasan ba sai dai Vinicius ne ya ci mata kwalli dayan. Kuma manema labarai sun tambaye shi cewa shin yana ran lashe kyautar Ballon D’or?
Sai yace masu tabbatas yana sa rai kuma a watan gobe zaije bugawa kasarsa ta Faransa wasa, amma baya jin cewa zai iya yin wani kokari sosai duk cewa dai bai san gaibu ba.
Amma yana alfahari da namijin kokarin da suka yi. Benzema ya kasance dan wasan mafi yawan kwallaye a gasar La Liga, da kuma Champions League bayan dayaci 15 a wannan kakar.