Tauraruwar fina-finan Hausa, Nafisa Abdullahi ta bayyana cewa, tauraron mawakin Hausa, Nazir Ahmad Sarkin Waka dan neman sunane.
Hakan na zuwa ne bayan da ya mayar da martani kan kiran da Nafisar ta yi na cewa a daina haihuwar yara ana barinsu a titi suna zama Almajirai.
Maganar ta Nafisa duk da wasu sun yaba mata amma wasu da yawa sun yi Allah wadai da ita.
Nazir Sarkin Waka a nasa martanin, ya fadi cewa, ba Almajirai ne iyayen su suka haifesu suka kasa kula dasu ba, idan kana neman ‘ya’yan da iyayen su suka haifa suka kasa kula dasu ro ka taho masana’ntar fim.
Wannan shine gaskiya malanmai
Ko tayi dadi ko kar tayi dadi..
Ayi hakuri damu! pic.twitter.com/64wVl4lBHK— Sarkinwaka (@real_sarkinwaka) April 22, 2022
Duk da yake bai kira Suna ba, wannan martani ne kai tsaye ga Nafisa, wadda ita kuma ta mayar masa da martanin cewa, dan neman sunane, ya kamata ya bugi kirji ya kira sunan da wa yake.
Ta kara da cewa, shima fa Nazir dinnan dan fim ne.
Tace amma jira yake ya samu dama sai ya rika maganganin shirme.
Clout chaser!!! Call names with your full chest now. I know what’s bothering you shaa 🚶♀️ 🚶♀️ Ramadan Kareem 🌙 https://t.co/2w6M99MH3v
— Nafisat Abdullahi (@NafisatOfficial) April 22, 2022
The attention seeking is sickening, he’s looking for any slight opportunity to open mouth and blab nonsense, he’s not even making sense.. the last time I checked, he’s a ‘ dan film’ too… ko yaki ko ya so! https://t.co/PEc9i4ktB8
— Nafisat Abdullahi (@NafisatOfficial) April 22, 2022
Wannan lamadai na ci gaba da daukar hankula a shafukan sada zumunta.