(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Tun da farko tsohon gwamnan jihar Borno Sanata Kashim Shettima ne ya fara kiran a gudanar da bincikekan harin.
A nasa bangaren kuma Sanata Ali Ndume da ke wakiltar Borno ta kudu ya ce “akwai sakaci, don haka nake goyon bayan kiran da Kashim Shetima ya yi cewa ya kamata a gudanar da bincike.
Sanatan ya kuma roki gwamnati ta taimaka wa wadanda suka yi hasara harin da aka kai a Auno.
“Girman barnar da aka yi a Auno ya wuce misali, mutum sai ya je ya gani da idonsa,” in ji Ndume.
Sanatan ya kuma yi kira ga shugaban kasa da jami’an tsaro su tausayawa mutanen Borno a kawo karshen rikicin da ya ce ya addabi Borno tsawon shekaru 10.
“Don Allah muna rokon gwamnati ta taimaka ta kawo karshen wannan matsalar ko da kuwa sojojin haya za ta dauko ta shigo da su Borno, idan zai taimaka a kawo karshen rikicin.”
“Muna nan muna binne mutanenmu ana muna barna kuma gwamnati tana da dama za ta iya magance wannan matsalar da ta addabe mu shekaru 10,” in ji shi.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Ku biyomu a shafukanmu na sada zumunta dan samun labarai masu kayatarwa:
A shafin twitter zaku same mu a @hutudole
A shafin Facebook zaku samemu a @hutudolehausa
Danna nan dan sanin yanda zaku tallata hajarku a shafin hutudole