fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

Rashin Imani:Yan bindiga sun kashe dan kasuwar da sukayi garkuwa da shi bayan sun karbi kudin fansa naira miliyan shida

Wasu yan bindiga sun jefa iyalan wani dan kasuwa, Yahaya Hassan Musa cikin bakin ciki bayan sun kashe shi duk da cewa sun karbi kudin fansa naira miliyan shida.

Yahaya Hassan nada aure da yara guda biyu kuma shi mazaunin jihar Kano ne. Yan bindigar sunyi garkuwa da shine a jihar Kogi yayin dawowarsa daga Kotono.

Kaninsa Abubakar Hassan Musa yace wan nasa a jirgin sama yake tafiya koda yaushe, amma kaddara tasa yabi mota a wannan karin. Abubakar ne ya kai masu kudin fansar inda suka fada masa inda zaiga dan uwan nasa amma yaje bai ganshi ba.

Karanta wannan  Labarin da muke samu yanzu na cewa 'yan bindiga sun kashe wani dan sanda a jihar Katsina yayin komawarsa gida daga aiki

Har kwana yayi a cikin dajin kafin daga baya wata mata da akayi garkuwa dasu tare ta fada masa cewa sun kashe shi. Hakan yasa yaje ya samo mafarauta suka nemo gawar suka binne shi a dajin saboda ba motar da zata dauki gawar don ta lalace sosai.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *