fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Rashin tsaro ne ke sa ba’a ganin ayyukan Shugaba Buhari – Ibinabo Dokubo

 

Wata ‘yar takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Ibinabo Dokubo, ta koka da yadda matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a kasar.

Matar wadda take fatan zama shugaban kasa ta ce rashin tsaro musamman a yankin Arewa maso Gabas da Arewa ta tsakiya ya sanya ‘yan Najeriya ba su ga dimbin nasarorin da gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC ta samu, musamman a fannin samar da ababen more rayuwa.

Ta yi wannan magana ne a lokacin da ta bayyana kudurinta na tsayawa takarar shugaban kasa jiya a Abuja.

Karanta wannan  Hotuna: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana sa Kwankwaso

Dokubo ta ce za ta nemi tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki tare da jiga-jigan jam’iyyar irinsu Bola Tinubu da Gwamna Yahaya Bello da sauran masu neman kujerar.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *