Jam’iyyar PDP ta gabatar da babban dan siyasa mai karfi da kuma dumbin masoya a arewanci Najeriya dama wasu sassan kudancin kasar, watau Atiku Abubakar a matsayin dab takarar shugaban kasa.
Amma sai dai tun a zaben fidda gwani suka fara takun saka da gwamna Wike bayan ya kayar da shi, sannan kuma Atiku yayi alkawarin bashi mataimaki amma sai yaba Okowa.
Aanda hakan yasa wasu jigajigan jam’iyyar ta PDP suka kalubalanci hakan har ma wasu ke cewa zasu sauya sheka.
Wanda hakan ka iya sawa burin da jam’iyyar take na doke APC a zabe mai zuwa yaja baya saboda matsalar da take fuskanta a cikin gida.