fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Sabon Rahoto me Ban tsoro: A gaba daya Duniya, Najeriya ce ta daya a yawan hare-haren kungiyar ISIS

Wani sabon Rahoto da wata kungiyar dake saka ido akan ayyukan ta’addanci ta Duniya ta fitar yace kungiyar ISIS da aka kafa a kasashen Iraqi da Syria, a yanzu hare-haren su yafi yawa a Najeriya.

 

Kungiyar dake Geneva a kasar Switzerland me suna jihad Analytics ta bayyana cewa,  tun daga fara shekarar 2022 hare-haren da kungiyar ISIS ta kai a Najeriya sun fi wanda ta kai a kasashen Iraqi da Syria yawa.

 

Kungiyar ISWAP itace wakiliyar kungiyar ISIS a yankin Afrika ta yamma kuma itace ke yada manufofin kungiyar ISIS din a Najeriya da kaddamar da hare-hare da sunanta.

Rahoton yace a karin farko tun bayan kafa kungiyar, Najeriya ta zama kasar da tafi kaiwa hare-hare.

 

Wannan dai manuniyace ga Shuwagabanni da kuma hukumomin tsaron Najeriya kan cewa su tashi tsaye wajan magance matsalar tsaro dan kar abin ya kara kazanta.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *