A dazu ne muka ji yanda Ministan harkokin kasashen waje, Geoffrey Onyeama ya bayyana cewa ya kamu da cutar Coronavirus/COVID-19 kuma ya tafi killace kanshi.
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari yayi mai addu’ar samun sauki. Shugaban a cikin wani sako daya fitar ta shafinshi na Twitter yace Ministan Mutumin Kirki ne kuma Najeriya tana gode masa saboda kokarin da yake.
I wish @GeoffreyOnyeama speedy recovery from Covid-19. Nigeria is eternally grateful for his diligence in attracting international support to defeat the pandemic and boost the economy. He has been a tireless worker and strong pillar of our administration.
— Muhammadu Buhari (@MBuhari) July 19, 2020
Shugaban ya bayyana cewa ministan yana kokari sosai wajan ganin an kawar da cutar Coronavirus/COVID-19 dan habaka tattalin arzikin Najeriya.