fbpx
Friday, June 9
Shadow

Shugaban kasar Amurka, Trump ya goyi bayan wata kungiya me nuna kiyayya ga musulmai: Hakan ya jawo mai Allah wadai

Shugaban kasar Amurka Donald J. Trump ya nanata wani sakon nuna cin zarafi da wata kungiyar masu tsattsauran ra’ayin kasar Ingila me suna Ingilace farko, sakon da kungiyar ta wallafa a dandalinta na sada zumunta da muhawara wanda ke dauke da wasu bidiyo dake nuna wasu mutane da ake kyautata zaton musulmaine sun kashe wani yaro sannan sun farwa wani nakasasshe kuma sun ruguza wani mutum-mutumi na kirista.


(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});

Donald Trump ya sake maimaita wannan sako a dandalinshi wanda hakan yake nuna cewa yana goyon bayan waccan kungiya, to saidai hakan be yiwa mutanen kasar, dama wasu na kasashen waje dadiba.

An bayyana saka wannan sako da Trump yayi a dandalinshi a matsayin goyon bayan cin zarafin musulmi da nuna kiyayya garesu.
Firaiministar Ingila Theresa May ta hannun me magana da yawunta tace bai kamata Trump ya wallafa wannan sako dake nuna kiyayya ga musulmai ba.
Amma maimakon ya saduda, sai Trump ya mayar mata da martani cewa kamata yayi ta mayar da hankali kan akidojin musulmai na ta’addanci dake barazana ga faruwar kasarta maimakon sukarshi.
Da yawa dai, musulmai da wadanda ba musulmai ba sunyi Allah wadai da wannan abu da Trump yayi.


(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});

Karanta wannan  Karfin Hali, Bidiyon yanda aka kama barawo a barikin sojoji

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *