fbpx
Friday, June 9
Shadow

Sojojin Najeriya sun harbe kwamandan kungiyar IPOB a jihar Imo

Dakarun Najeriya da ke da alaka da birgediya ta 34 sun kashe wani dan bindiga da aka bayyana amatsayin Kwamandan masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) a Imo.

Sojojin sun ce sun ci karo da ‘yan kungiyar ‘yan awaren, inda suke ta harbe-harbe a mahadar ayaba da ke karamar hukumar Orlu a jihar.

An ce suna aiwatar da umarnin “zama-gida ba bisa ka’ida ba” kan ‘yan ƙasa masu bin doka.

Kakakin rundunar, Brig.-Gen. Onyema Nwachukwu, ya bayyana a cikin wata sanarwa a Abuja ranar Litinin cewa an kashe dan bindigar ne a yayin wata fafatawar da aka yi a yankin Ihioma a Orlu.

Karanta wannan  Bayan Kwashe kusan watanni 6 tana karyatawa a karshe dai, Hukumar Sojojin Saman Najariya ta amince da kuskuren harba bamabaman da suka kashe farar hula 39 a jihar Nasarawa

Nwachukwu ya ce a lokacin da suka ga sojojin, ‘yan kungiyar IPOB/ESN sun janye a cikin wata babbar mota kirar Toyota Highlander blue zuwa yankin Ihioma domin karfafa musu gwiwa.

A rikicin da ya barke, an damke daya daga cikin masu laifin, yayin da wasu suka gudu cikin rudani. Dakarun na ci gaba da yin katsalandan a yankin gaba daya a ci gaba da gudanar da aikin zakulo ‘yan ta’addar da suka tsere.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *