
Zaka iya yin komai kasha amma muddin ka zubar da jinin mutum koda ba Musulmi bace wallahi Allah ba zai barka ba>>Sarkin Katsina
Me martaba Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumin Kabir Usman ya bayyana cewa akwai makiyan shugaban Kasa,Muhammadu Buhari dake tare dashi da kuma na waje dake son lalata Arewa wanda yace shune ke daukar nauyin hare-haren dake faruwa a yankin.
Ya bayyana hakane jiya a fadarsa yayin da tawagar gwamnatin tarayya ta kaimai ziyarar bangirma busa jagirancin me baiwa shugaban kasar shawara kan harkar tsaro, Janar Babagana Mungono me ritaya.
Sarkin yace suna godiya da ziyarar da wakilan gwamnatin tarayyar suka kai yace amma fa ya sha gayawa shugaban kasa,Muhammadu Buhati yayi hankali da makiyan dake tare dashi dana nesa wanda sunaso su lalata gwamnatinsa da kuma Arewa. Yace duk wanda ya lalata shugaba Buhari ai ya lalata Arewane baki daya dama Najeriya.
Yace babu masar...