fbpx
Saturday, March 25
Shadow

Tag: Africa ta Kudu

Hotuna: Soja ya dirkawa wani matashi harsashi saboda bai saka takunkumin rufe baki da hanci ba

Hotuna: Soja ya dirkawa wani matashi harsashi saboda bai saka takunkumin rufe baki da hanci ba

Tsaro, Uncategorized
Wani soja a kasar Yankin Mogwadi, Limpopo dake kasar Africa ta kudu ya dirkawa wani matashi, dan shekaru 27 harsashi yayin da gaddama ta kaure tsakanin akan dalilin da yasa matashin bai saka takunkumin rufe baki da hanci ba.   Kakakin 'yansanda, Motlafela Mojafole ya bayyana cewa lamarin ya farune ranar 17 ga watan Satuma, watau, Jiya kenan.   Yace am kama sojan inda ake zarginsa da kisan ganganci yayin da shi kuma wanda aka harba din aka garzaya dashi Asibiti.
Kabusai Sun Shanye Gabadayan Tabar Sigari A Kasar Afrika Ta Kudu

Kabusai Sun Shanye Gabadayan Tabar Sigari A Kasar Afrika Ta Kudu

Kiwon Lafiya
Rahotanni daga kasar Afrika ta Kudu sun ce hamshakan kabusai sun karar da ilahirin kararen taba sigarin da suka samu kaiwa gare su, a shagunan dake sassan kasar. Mabusa taba sigari a Afrika ta Kudun sun bazama zuwa shagunan sayar da sigari ne, bayan da gwamnati ta janye dokar haramta sayar da tabar da ta shafe watanni 5 tana aiki, domin dakile yaduwar annobar coronavirus ta hanyar hana cinkoson jama’a.   Tun a ranar Asabar da ta gabata, 15 ga watan Agustan da muke ciki shugaban Afrika ta Kudu, Cyril Ramaphosa ya sanar da janye dokar hana sayar da tabar, da ma barasa a sassan kasar, matakin da ya soma aiki a ranar Litinin da ta gabata. Bayanai sun ce fargabar cewa kila gaba gwamnati ta sake maido da dokar ya sanya dubban jama’a tururuwa zuwa shagunan sayar da taba sigar...
Adadin Wadanda Suka Kamu Da COVID-19 a Afrika Ta Kudu Ya Zarta 500,000

Adadin Wadanda Suka Kamu Da COVID-19 a Afrika Ta Kudu Ya Zarta 500,000

Kiwon Lafiya
A ranar Asabar 1 ga watan Agusta adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 ya zarta 500,000 a Afrika ta kudu, adadin da ya zama kaso 50 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar da aka sani a kasashen Afrika 54.   A daren ranar Asabar ministan ma’aikatar lafiya na kasar Zwelini Mkhize ya sanar da cewa an samu karin mutum 10,107 da suka kamu da cutar, abinda ya sa gaba dayan adadin yanzu ya kai 503,290, ciki har da mace-mace 8,153. Afrika ta kudu, mai yawan jama’a kusan miliyan 58, ita ce kasa ta 5 a lissafin kasashen da cutar ta fi kamari a duniya, bayan Amurka sai Brazil, Rasha da India, dukkansu kasashe ne da ke da yawan al’umma, a cewar jami’ar Johns Hopkins. Kwararru sun ce ainahin adadin wadanda suka kamu da cutar a fadin duniya ya wuce wanda aka tabbatar,...