fbpx
Saturday, March 25
Shadow

Tag: Africa

Mane ya taimakawa Senegal ta zama kasa ta farko data cancanci buga gasar cin kofin Nahiyar Africa

Mane ya taimakawa Senegal ta zama kasa ta farko data cancanci buga gasar cin kofin Nahiyar Africa

Wasanni
Dan Kwallon kafar kasar Senegal me bugawa kungiyar Liverpool wasa, Sadio Mane ya taimakawa kasarsa da kwallo wadda suka samu nasara akan Guinea Bissau da 2-0.   Da wannan nasara, Senegal ta samu kaiwa ga buga gasar Cin kofin Nahiyar Africa a 2022.   A mintuna 82 ne Mane ya saka kwallon data basu nasara wanda a yanzu suna da maki 12 kenan.  
Zamu taimakawa ci gaban Dimokradiyya a Africa>>Shugaba Buhari

Zamu taimakawa ci gaban Dimokradiyya a Africa>>Shugaba Buhari

Uncategorized
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa Najeriya zata taimakawa ci gaban Dimokradiyya a Nahiyar Africa.   Shugaban ya bayyana hakane a yayin da yake karbar bakuncin shugaban kasar Burkina Faso, Roch Marc Christian Kabore a fadarsa dake Abuja.   Shugaban ya bayyana cewa, duk kasar dake shirin zabe, Najeriya zata taimaka mata wajan ganin an yi nasa a zaben yace suna saka ido sosai kan kasashen Africa da harkar zabukansu. A nasa bangaren shugaban kasar Burkina Faso ya bayyana cewa ya zo Najeriya ne a ziyarar kwana daya dan su tattauna matsalolin kasuwanci dake tsakanin kasashen. Ya kuma jinjinawa shugaba Buhari akan yaki da ta'addanci da kuma yanda yake yaki da cutar Coronavirus/COVID-19.
Kasar Amurka ta yi gargadin kungiyoyin ‘yan ta’adda na ISWAP da Al-Qaeda na mamaya a Africa

Kasar Amurka ta yi gargadin kungiyoyin ‘yan ta’adda na ISWAP da Al-Qaeda na mamaya a Africa

Tsaro
Kasar Amurka ta bayyana cewa sai kasashen Africa sun dage da kuma kula da yanda zasu yi maganin 'yan ta'adda saboda manyan kungiyoyin 'yan ta'adda na Duniya, ISIS da Al-Qaeda na kwarara cikin yankin Africa ta yamma.   Wani janar din kasar Amurka dake kula da yanayin tsaron Africa, Janar Davin Anderson ne ya bayyana haka a ganawar da yayi da manema labarai. Yace kungiyoyin sun shiga kasashen Mali da Burkina Faso suna mamaye gurare tare da karbar haraji.   Yace bayan yin galaba akansu a kasashen Syria da Iraqi, sun zabi shiga kasashen Africa saidai basa bayyana kansu, suna ayyukansu ne a boye.
Masu Cutar Corona A Afrika Sun Kai Mutane 612,586>>Cibiyar Kula Da Cututtuka Ta Afrika

Masu Cutar Corona A Afrika Sun Kai Mutane 612,586>>Cibiyar Kula Da Cututtuka Ta Afrika

Uncategorized
A ranar Laraba ne Cibiyar Kula da Yaduwar Cututtuka ta Afrika CDC ta bayyana cewa, a halinn yanzu akwai masu fama da cutar korona 612,586 a nahiyar Afrika. Cibiyar ta bayana haka ne a sakon da ta wallafa a shafin ta na tiwita ranar Laraba in da ta ce, yawan masu cutar ya tashi daga 594,841 a ranar Talata zuwa 612,586 a ranar Laraba da safe. Cibiyar ta kuma bayyana cewa, cutar ta kashe mutum 13,519 a kididdigar da aka yi a wannan lokacin. An kuma samu nasara wakewar mutum 307,069 da suka kamu da cutar tunda farko. Bayani ya kuma nuna cewa, kasar Afrika ta Kudu ce cutar ta fi addaba daga nan kuma sai kasashen Egypt, Nigeria, Ghana, Algeria, Morocco, da kuma kasar Cameroon. Kidididgar ta kuma nuna cewa, yankin Afrika ta Yamma ce ya fi fama da cutar daga nan kuma sai kum...
Mutane 300,000 zasu iya Mutuwa sanadin Coronavirus/COVID-19 a Africa>>UN

Mutane 300,000 zasu iya Mutuwa sanadin Coronavirus/COVID-19 a Africa>>UN

Kiwon Lafiya
Ofishin kula da tattalin Arzikin Africa na majalisar Dinkin Duniya,UNECA a sabon Rahoton daya fitar kan cutar Coronavirus/COVID-19 ya bayyana cewa mutane Dubu 300 zasu iya mutuwa Sanadiyyar cutara Africa.   Rahoton wanda kamfanin dillacin Labaran Najeriya ya samu ya kuma ce lamarin cutar zai jefa mutane Miliyan 27 cikin Tsananin Talauci.   Rahoton yace akwai bukatar samar da kudi, Dala Biliyan 100 dan baiwa Aftica tallafi.   Ya kuma koka kan rashin kyawun tsarin lafiya a Nahiyar.
Dangote zai Kashe Milliyan 200 don yaki da cutar coronavirus a Najeriya

Dangote zai Kashe Milliyan 200 don yaki da cutar coronavirus a Najeriya

Kiwon Lafiya
Gidauniyar Aliko Dangote (ADF) ta dauki alkawarin Naira miliyan 200 don tallafawa kokarin Gwamnatin Tarayya akan dakile yaduwar cutar Covid-19 (CoronaVirus) a kasar. Ms Zouera Youssoufou, Babbar Darakta a Gidauniyar Aliko Dangote, a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata a Legas, ta ce bayar da gudummawar wani bangare ne na manufar gidauniyar.  Youssoufou ta bayyana cewa, an ware kudi kimanin  miliyan N124 don tallafawa wuraren da za su taimaka wajen dakile sake bullar cutar da kayan aiki, musamman guraran shige da fuce na kasa, A cewarta, burin gidauniyar dangote shine taimakawa gwamnati, wajan Samar da ingattaccen kiwon lafiya ga yan kasa. Akwai kuma Miliyan 36 da aka ware wajan yin aikin binciken masu dauke da cutar sannan akwai kuma miliyan 48 itama da za'a y amfan...