fbpx
Sunday, March 26
Shadow

Tag: Almajiranci

An kama wata kungiyar mutane 10 da suka kware wajan yiwa yara, Maza, hadda almajirai Fyade a jihar Taraba

An kama wata kungiyar mutane 10 da suka kware wajan yiwa yara, Maza, hadda almajirai Fyade a jihar Taraba

Uncategorized
A jihar Taraba an kama wasu mutane 9 tare da wani dan kasuwa wanda suka kware wajan yiwa kananan yara maza,Fyade.   Me magana da yawun 'yansandan jihar, DSP David Misal ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace nan gaba kadan zasu gurfanar da masu laifin a gaban kuliya. 'Yan sintirin unguwane dai suka kama Wani Umar Isa a Jalingo a wani kango yana lalata da wani karamin yaro da bai wuce shekaru 10 ba.   Daga nanne sai aka gano mutane 10 wanda kungiya garesu da suka kware wajan lalata yara maza ciki hadda almajirai.
Rikon sakainar kashin da manyan Arewa Musulmai suka yi wa yankin ya haifar da Almajirai>>Kukah

Rikon sakainar kashin da manyan Arewa Musulmai suka yi wa yankin ya haifar da Almajirai>>Kukah

Uncategorized
Babban Limamin Cocin Katolika, Rabaren Hassan Kukah ya bayyana cewa irin rikon sakainar kashin da manyan Arewa Musulmai suka yi wa yankin ya haifar da almajirai dake gararamba a yankin.     Kuka ya ce tun farko wannan tsari na karantar da yara ya samu asaline daga kalmar Muhajirun, kuma da shine aka tsara wannan karantarwa tun a abaya, saidai daga baya an gurbata tsarin ta yadda maimakon a yi nasara ci baya aka samu.     Ya shaida cewa lallai lokaci yayi da za a yi watsi da wannan tsari na Almajirci, kowani da yayi karatu a gaban iyayen sa, sannan ya shiga makarantar Boko.     ” Koda yake fadin haka da gwamnoni suka yi kamar burma wa kai wuka  ne, domin kowa ya sani cewa tsarin almajirci ya...
Jihohin Arewa 4 da sukace ba zasu kori Almajirai ba

Jihohin Arewa 4 da sukace ba zasu kori Almajirai ba

Uncategorized
Maganar korar almajirai su koma jihohinsu na Asali da gwamnonin Arewa suka cimma matsaya akansa ya dauki hankula sosai inda wasu suka goyi baya, wasu kuma suna nuna rashin goyon bayan wannan batu.   Saidai duk da cimma matsayar da gwamnonin suka yi, wasu jihohin Arewar sun ki mutunta waccan yarjejeniya. Hutudole ya kawo muku jihohi 4 da suka ce ba zasu kori Almajirai ba kamar haka:   Jihar Borno:   Jihar Borno kusan za'ace tana dsya daga cikin jihohin dake gaba-gaba wajan karbar Almajirai a Najeriya tun tale-tale zaka ji ana cewa akai wane gabas.   Gwamna Babagana Umara Zulum ya cimma matsaya cewa ba zai kori Almajirai zuwa jihohinsu na Asali ba, zai zamanantar da Lamarin karatun nasu.   Jihar Yobe:   Jihar Yobe dake ...
Hotunan Ban Tausai:’Yan sanda sun kama malamin da ya yi wa almajiransa mugun duka

Hotunan Ban Tausai:’Yan sanda sun kama malamin da ya yi wa almajiransa mugun duka

Uncategorized
'Yan sanda sun kama wani malamin makarantar allo a jihar Diffa da ke kudu maso gabashin jamhuriyar Nijar bayan an zarge shi da yi wa almajiransa dukan kawo wuƙa.     Tuni dai, mahukunta suka kwashe almajiran inda suka kai su asibiti. Bayanai dai sun ɗaliban suna can kwance suna shan magani.     Mazaunan garin Diffa sun riƙa yaɗa wasu hotuna a shafukan sada zumunta da ke nuna wasu ƙananan yara tuɓe babu riguna, wasu daga ciki an ga bayansu duk a farfashe da alamun duka.   Yayin da wasu kuma dukan har ya shafi fuskokinsu, ga kuma baki a kukkumbure.     Wani shaida da ya zanta da BBC kan wannan lamari, ya ce yana cikin tafiya wani yaro ya taho da gudu yana neman agaji daga gare shi. "Na ga gudan ba kyau, (halin da yake ciki...
Idan Har Za A Kashe Almajiranci To Shi Ma Karatun Boko A Kashe Shi>>Sheik Aliyu Adarawa

Idan Har Za A Kashe Almajiranci To Shi Ma Karatun Boko A Kashe Shi>>Sheik Aliyu Adarawa

Uncategorized
Babban malamin addinin musulunci a Nijeriya kuma shugaban majalisar malammai na Jihar Neja, Sheik Aliyu Muhammad Sani Adarawa ya bayyana takaicin sa akan yadda gwamnati da wasu gwamnoni suka fi maida hankali akan kashe almajiranci maimakon zamanantar da tsarin karatun.     Malamin ya bayyana hakanne a lokacin da yake rufe tafsirin da yake gabatarwa a garin Kontagora dake Jihar Neja a yau laraba, Sheik Adarawa ya ce " Kashe tsarin almajiranci da gwamnati ke ƙoƙarin yi ba adalci bane, domin suma almajirai ƴan ƙasa ne kamar kowa suna da ƴancin zuwa duk garin da suke so domin neman ilimi kamar yadda kowani ɗan Najeria keda shi.   Sheik Aliyu adawarawa ya ƙara da cewar "Idan har za'a bar ƴan boko suje wasu sassan Najeria harda ƙasashen waje neman ilimi kuma kar...
Kun ci Amanar Almajirai kuma kun mayar da ‘yan Najeriya kamar ba mutane ba>>PDP ta gayawa APC

Kun ci Amanar Almajirai kuma kun mayar da ‘yan Najeriya kamar ba mutane ba>>PDP ta gayawa APC

Siyasa
Jam'iyyar Hamayya ta PDP ta zargi jam'iyya me mulki ta APC da cewa ta ci amanar 'yan Najeriya da Almajirai bayan ta yi amfani dasu ta cimma burinta na hawa mulki.   Akwai dai rahotanni da a yanzu haka suke ta kara fitowa kan yanda gwamnonin jihohin Arewa ke mayar da Almajirai jihohinsu na Asali sannan kuma ana kama motoci cike da Almajiran a wasu jihohin Kudu inda ake mayar dasu inda suka fito.   A Sanarwar data fitar ta hannun sakataren watsa labaranta, Kola Ologbondiyan PDP ta bayyana cewa shugaba Buhari da gwamnatinsa sun lalata duk wani aikin Alherin da ta fara yiwa 'yan Najeriya a cikin shekaru 5 da suka shafe suna mulki.   PDP tace an mayar da 'yan Najeriya saikace ba mutane ba,harkar tsaro ta tabarbare,Buhari da yace zai jagoranci yaki da Boko Ha...
Bayan Haramta Almajiranci Ya Kamata A Haramta Karuwanci

Bayan Haramta Almajiranci Ya Kamata A Haramta Karuwanci

Uncategorized
Shugabanni suna ta kokarin haramta almajiranci da bara a arewacin Nigeria musamman a dalilin zuwan wannan cuta na Coronavirus, har ma ana cewa Almajirai suna yada cutar Coronavirus, amma ba mu ga wani yunkuri da sukeyi na daukar mataki a kan Karuwai da gidajen karuwai ba.     Muna goyon bayan a haramta bara dari bisa dari, domin bara baya daga cikin tsarin karantarwan Musulunci, bara kaskanci ne, amma bama goyon a hana Almajiranci, ayi doka duk wanda zai tura yaranso Almajiranci to ya dauki nauyin cinsa da shansa da sutura, Almajirin da akaga yana bara a kamashi a kuma rufe tsangayar da yake karatu.     Kuma muna jawo hankalin masu iko yadda ake ta kwashe almajirai daga jihohi ana mayar dasu inda suka fito ya kamata a haramta karuwanci a rufe duk w...
“Gwamnatin Jihar Yobe Ba Za Ta Kori Almajirai Daga Jihar Ba”

“Gwamnatin Jihar Yobe Ba Za Ta Kori Almajirai Daga Jihar Ba”

Uncategorized
Shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin jihar Yobe, Honarabul Abdullahi Yusuf Opera, ya bayyana cewa Gwamnatin jihar Yobe ba za ta kori Almajirai daga fadin jihar ba.     Opera ya yi jawabin ne a hirar shi da 'yan jaridu a fadar Gwamnatin jihar Yobe, inda ya bayyana cewa, jihar Yobe da Borno sune cibiyar koyar da karatun addinin Musulinci na Tsangaya.     A jawaben nasa, ya bayyana cewa, yanzu haka gwamnatin jihar Yobe ta karbi Almajirai guda 125 daga jihar Gombe, a jiya Alhamis ma An kawo Almajirai guda 52, daga jihar Nasarawa, a wani mataki na gujewa yaduwar Annobar Cutar Corona-Virus, duk an killace Almajiran a Sansanin yan Bautar kasa dake Dizigau (NYSC CAMP) da GSSS Damaturu.     Gwamnatin jihar Yobe, karkashin jagoranci Gwamna,...
Hotuna:Jihar Kaduna ta tare motoci cike da Almajirai da matasa 108 sa suka yi yunkurin shiga jihar

Hotuna:Jihar Kaduna ta tare motoci cike da Almajirai da matasa 108 sa suka yi yunkurin shiga jihar

Siyasa
Jihar Kaduna ta tare motoci cike da Almajirai da matasa su 108 wanda suka taso da Abuja da niyyar shiga cikin Kaduna.   Tuni dai aka taresu sannan aka kaisu Hajj Camp inda za'a killacesu.   Gwamnatocin jihohi da dama na daukar irin wannan mataki na hana matafiya shiga jiharsu musamman a wannan yanayi da ake ciki na fama da Annobar cutar Coronavirus/COVID-19. https://twitter.com/KDHSSD/status/1257710768793047042?s=19 Almajirai da yawane da aka mayarwa Kaduna daga Kano suka kamu da cutar.
CORONAVIRUS: Kungiyar Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Haramta Almajiranci A Arewacin Nijeriya

CORONAVIRUS: Kungiyar Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Haramta Almajiranci A Arewacin Nijeriya

Uncategorized
Kungiyar gwamnonin Arewa ta daga kan cewa ya zama dole a haramta Almajiranci a yankin kamar yadda The Punch ta ruwaito.     Gwamnonin sun bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da suke tattaunawa kan matakan da yankin za ta dauka don yaki da annobar coronavirus.     Shugaban kungiyar, Gwamna Simon Lalong na jihar Filato ne ya jagoranci taron da gwamnonin 17 suka gudanar ta hanyar amfani da intanet.     Gwamnonin sun kuma tattauna hatsarin da Almajirai ke ciki sakamakon bullar coronavirus inda dukkansu suka amince a haramta almajiranci kuma a mayar da yaran zuwa gidajen iyayensu ko jihohinsu na asali.     Sun dau alwashin cewa ba za su bari a cigaba da almajirancin ba, duba da irin kallubalen da ya ke haifar wa da su...