
Kasar China na yunkurin rage yawan Musulmin
Manufofin kasar China na mayar da dubban 'yan kabilar Uighur da sauran kananan kabilu a birnin Xinjiang zuwa sabbin wuraren ayyuka nesa da gida yana haifar da raguwar yawansu, kamar yadda wani cikakken bincike na kasar China da BBC ta gano ya nuna.
Gwamnati ta musanta cewa tana yunkurin sauya alkaluman yawan al'ummar yankinta na yammaci mai nisa, sannan ta ce sauye-sauyen wuraren aikin an tsara ne saboda samar da kudaden shiga da kuma shawo kan matsalolin rashin aikin yi da talauci.
Amma bincikenmu ya nuna cewa - hade da sansanonin sake ilimantarwa da aka kafa a fadin birnin Xinjiang a shekarun baya - manufofin sun kunshi babbar barazanar tursasawa kana an kuma tsara ne don a sauya wa kananan kabilu tunani da kuma tsarin tafiyar da rayuwarsu.
Binciken, wanda ak...