fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

Tag: Coronavirus/COVID-19 Nigeria

Yawan Masu Coronavirus/covid-19 ya zarta Miliyan 20 a Fadin Duniya

Yawan Masu Coronavirus/covid-19 ya zarta Miliyan 20 a Fadin Duniya

Kiwon Lafiya
Rahotanni sun bayyana cewa, yawan masu cutar Korona a fadin Duniya sun zarta Milliyan 20. A daran Ranar Lahadin data gabata adadin yawan masu fama da cutar ya karu, inda yawan masu cutar ya kai kimanin 20,016,286, yayin da kimanin mutane 733,592 suka mutu sakamakon cutar coronavirus a fadin Duniya. Ya zuwa yanzu  kasashe guda Uku ne, cutar tafi ta'azzara, wadanda  suka hada da kasar Amurka, Brazil sai Kasar India.  
Gwamnatin tarayya ta ba da Umarnin tilasta Yin amfani da Takun-kumin rufe hanci a duk fadin kasar

Gwamnatin tarayya ta ba da Umarnin tilasta Yin amfani da Takun-kumin rufe hanci a duk fadin kasar

Kiwon Lafiya
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci gwamnatocin jihohi da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja (FCT) da su aiwatar da amfani da Takun-kumin rufe hanci a wuraren jama'a a fadin kasar. Shugaban Kwamitin kan cutar COVID-19, Mista Boss Mustapha ne ya sanar da hakan a taron tattaunawar yau da kullun dake gudana a Abuja a ranar Alhamis. Boss Mustapha, ya bayyana hakan ne a yayin da yake bita kan ayyukan kwamitin, ya ce shugaban ya kuma amince da saukaka dokar kulle har tsawan sati 4. Shugaba Buhari ya kuma nemi PTF da ta hada gwiwa da jihohi da kananan hukumomi don inganta wayar da kan al’umma game da cutar. "Ya kuma karfafa gwamnatocin jihohi da su hada hannu da hukumomin kananan hukumomi don kara daukar matakan da suka wajabta na kariya kamar su rage cunkosu, sanya takukumi, da ts...
An samu karin sabbin mutum 481 wanda suka harbu da Coronavirus/covid-19 a Najeriya

An samu karin sabbin mutum 481 wanda suka harbu da Coronavirus/covid-19 a Najeriya

Kiwon Lafiya
Cibiyar dakile yaduwar cututtuka NCDC ta sake fidda sanarwar kara samun adadin mutum 481 wanda suka harbu da cutar coronavirus a fadin kasar. Sanarwar wanda hukumar ta wallafa ta cikin shafinta dake kafar sadarwa a ranar Alhamis 29 ga watan Yulin shekara ta 2020. Haka zalika hukumar ta zayyana jahohin da aka samu karin masu cutar wadanada suka hada da: https://twitter.com/NCDCgov/status/1288962552282656768?s=20 Bayan haka cibiyar ta bada rahoton sallamar adadin mutum 19,270 sannan kuma an samu.mutuwar mutum 878 a fadin kasar.
‘Kashi 63% na sinadaran tsaftar hannu don kariya daga cutar Korona da a ke amfani dasu a Abuja basu da rijistar NAFDAC >> Boss Mustapha

‘Kashi 63% na sinadaran tsaftar hannu don kariya daga cutar Korona da a ke amfani dasu a Abuja basu da rijistar NAFDAC >> Boss Mustapha

Kiwon Lafiya
Sakataren Gwamnatin Tarayya kuma Shugaban Kwamitin Shugaban kasa kan yaki da cutar COVID-19, Boss Mustapha, a ranar Alhamis ya ce wani bincike da Cibiyar Nazarin Magunguna ta Najeriya ta yi don duba yawan abubuwan da ke shigowa cikin kasuwa, ya nuna cewa Kashi 63 cikin dari na sinadaran tsabtace hannu wanda aka fi sani da Sanitizer da ake amfani dasu a Abuja basu da lambar rajista ta NAFDAC. Dan haka kwamitin ya shawarci 'yan Najeriya dasu guji samarwa ko amfani da kayayyakin da zasu iya yin illa ga jama'a.  
Bayan samu sabbin mutum 561 cutar coronavirus ta zarta 25,000

Bayan samu sabbin mutum 561 cutar coronavirus ta zarta 25,000

Kiwon Lafiya
Cibiyar dakile yaduwar cututtuka NCDC ta sake fidda sanarwar kara samun adadin mutum 561 wanda suka harbu da cutar coronavirus a fadin kasar. Sanarwar wanda hukumar ta wallafa ta cikin shafinta dake kafar sadarwa a ranar talata 30 ga watan Yunin shekara ta 2020. Haka zalika hukumar ta zayyana jahohin da aka samu karin masu cutar wadanda suka hada da: Lagos-200 Edo-119 Kaduna-52 FCT-52 Niger-32 Ogun-19 Ondo-16 Imo-14 Plateau-11 Abia-8 Oyo-8 Bayelsa-7 Katsina-6 Kano-5 Bauchi-3 Osun-3 Kebbi-3 Borno-2 Jigawa-1 Bayan haka cibiyar ta bada rahoton sallamar adadin mutum 9,746 sannan kuma an samu.mutuwar mutum 590 a fadin kasar
Covid-19: An bude filin tashi da saukar jiragen sama na Nnamdi Azikiwe dake Abuja

Covid-19: An bude filin tashi da saukar jiragen sama na Nnamdi Azikiwe dake Abuja

Kiwon Lafiya
Filin saukar jirgin saman Nnamdi Azikiwe, dake Abuja an sake bude shi a ranar Asabar, don cigaba da zirga zirga. Filin jirgin saman ya kuma tsaurara matakan tsaro, da nufin rage yaduwar cutar coronavirus. Kamfanin Dillancin Labarai na (NAN), ya ba da rahoton cewa an yi tanadin kayan wanke hannu, tare da guraran gwajin, don kare mutane daga kamuwa da cutar covid-19. Haka zalika an kuma sake tsarawa tare da shirya kujerun da suka kasance a cunkushe domin aiwatar da tsarin bada tazara juna. Idan zaku tuna cewa Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA), a makwannin da suka gabata, ta ce filin jirgin saman zai sake budewa don cigaba da zirga zirga a ranar 27 ga Agusta, bayan daukan  watanni a rufe a sakamakon barkewar cutar Coronavirus.
Kuma dai: Gwamnati ta sake fitar da sabbin dokokin da za’a bi kamin bude makarantu

Kuma dai: Gwamnati ta sake fitar da sabbin dokokin da za’a bi kamin bude makarantu

Siyasa
Ministan Ilimi,Adamu Adamu ya gabatarwa da majalisar tarayya da wasu sharudda da suka saka wanda sai kowace makaranta ta bisu kamin a barta ta bude ta ci gaba da koyarwa.   Ministan ya bayyana cewa ganin cutar Coronavirus/COVID-19 bata da Niyyar tafiya nan kusa yasa suka fitar da wadannan sharuda wanda an fitar dasu ne bisa shawarar kwararru da kuma masana akan harkar Ilimi. Yacs an gabatarwa da majalisar sharidanne dan ta duba ta gani tare sa shaida halin da ake ciki.   Daga cikin sharudan shine sai kowace makaranta ta samar da wajan killace masu Coronavirus/COVID-19 na wucin gadi. Sannan sai kowace makaranta ta samar da tsarin bada agajin gaggawa da kuma kawar da wanda cutar Coronavirus/COVID-19 ta kama nan take.
Masallatai na bin dokokin Coronavirus/COVID-19 sau da kafa>>Majalisar Koli ta Addinin Musulunci ta tabbatarwa da gwamnatin tarayya

Masallatai na bin dokokin Coronavirus/COVID-19 sau da kafa>>Majalisar Koli ta Addinin Musulunci ta tabbatarwa da gwamnatin tarayya

Uncategorized
Majalisar koli ta addinin Musulunci a Najeriya, NSCIA da kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN sun bayar da tabbacin cewa Musulmai da Kiristoci na bin dokokin da gwamnati ta zayyana na dakile yaduwar cutar Coronavirus/COVID-19 a Coci-coci da Masallatai.   Hakan na zuwane bayan da gwamnatin tarayya ta koka kan cewa wasu guraren ibadar sun fatali da dokokin da gwamnati ta saka na hana yaduwar cutar. Me magana da yawun majalisar koli ta addinin Musulunci,  NSCIA, Aselemi Ibrahim ya bayyana cewa, basu ji dadin wannan magana ta gwamnati ba domin a farko sunce kowa yayi Sallah a gida amma daga baya sai suka bada shawarar duk masallacin da zai bude ya tabbatar cewa an tanadi kiyaye  dokokin hana yaduwar cutar Coronavirus/COVID-19.   Shima sakataren CAN, Joseph Daramola ya...
Cutar coronavirus a Najeriya ta cimma 20,000 bayan samun karin mutum 436

Cutar coronavirus a Najeriya ta cimma 20,000 bayan samun karin mutum 436

Kiwon Lafiya
Cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta Najeriya ta fitar da sanarwar Kara samun sabbin wadanda suka kamu da cutar har mutum 436, Wanda adadin ya zarta dubu 20. Hutudole ta rawaito daga shafin hukumar wanda ta wallafa sanarwar karin a ranar lahadin data gabata.   Haka zalika cibiyar ta lasafta jahohin da aka samu karin da ya hada da: Lagos-169 Oyo-52 Plateau-31 Imo-29 Kaduna-28 Ogun-23 FCT-18 Enugu-18 Bauchi-17 Bayelsa-14 Rivers-8 Osun-6 Kano-6 Edo-5 Benue-5 Adamawa-3 Borno-2 Abia-1 Ekiti-1. https://twitter.com/NCDCgov/status/1274832787393167361?s=20   Cibiyar ta kuma bayyana adadin mutum 6,879 da aka sallama bayan samun mutuwar mutum 518.  
Covid-19: Najeriya ta sake samun karin mutum 661 yayinda adadin wadanda suka mutu ya kai 506

Covid-19: Najeriya ta sake samun karin mutum 661 yayinda adadin wadanda suka mutu ya kai 506

Kiwon Lafiya
A rahoton da Hutudole ta rawaito daga cibiyar yaki da cututtuka ta Najeriya ya nuna cewa an samu karin mutum 661 wanda suka harbu da cutar coronavirus a fadin kasar. Cibiyar yaki da Cututtuka ta Najeriya ta sanar da hakan ne a cikin wani sakon Tuwita data wallafa a ranar Asabar. Cibiyar ta ce sabbin wadanda suka kamu da cutar sun kamu a cikin jihohi 14 ciki har da Babban birnin tarayya Abuja. Lagos-230 Rivers-127 Delta-83 FCT-60 Oyo-51 Edo-31 Bayelsa-27 Kaduna-25 Plateau-13 Ondo-6 Nasarawa-3 Ekiti-2 Kano-2 Borno-1. https://twitter.com/NCDCgov/status/1274469457851793409?s=20 Rahoton Hutdole sun nuna cewa an gudanar da gwajin mutum akalla 111,052 yayin da aka tabbatar da mutum  12,584 wadanda suka harbu da cutar COVID-19.