fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Tag: Enugu

Farashin Manja yayi Gwauran zabi A wasu sassan kusawanni

Farashin Manja yayi Gwauran zabi A wasu sassan kusawanni

Kasuwanci
Rahotanni na nuni da cewa, an samu hauhawar farashin Manja a wasu manyan kasuwanni dake ciki da wajan jihar Enugu da ke kudancin Najeriya kamar yadda kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya rawaito. A rahotan da Kamfanin Dillancin labaran ya gabatar ya bayyana cewa, Farashin Manjan ya karu da kusan kaso 25, idan a ka kwatanta shi da kwanakin baya. Farsahin manjan a wasu kasuwanin jihar da su ka hada da, Akwata Garki, da Mayor ya kai 5,000 a kan kowanne galan wanda ada ake sayar dashi a kan farashin Naira 2,900. Hakanan kowacce kwallaba ake sayar da ita akan Naira 700 mai makon 500, yayin da ko wacce jarka ake sayar da ita akan farashin Naira Dubu 25 ko 24.
Wani Mutum ya yiwa mahaifinsa kisan gilla da gatari a Enugu

Wani Mutum ya yiwa mahaifinsa kisan gilla da gatari a Enugu

Uncategorized
Wani dan shekara 64, William Ogbu, wanda dan sa ya kashe a garin Aji da ke karamar hukumar Igbo Eze ta Arewa a jihar Enugu.   Marigayi William Ogbu yana da yara biyar da suka girma ciki har da maza biyu da mata uku.  Johnson Ogbu ne ya kashe shi da gatari kimanin kwanaki uku da suka gabata kuma aka binne shi a cikin wani kabari mara zurfi kusa da gonar ayaba kusa da gidansa na Umuidenyi. An ce Johnson ya yi fama da matsalar tabin hankali amma daga baya hankalinsa ya dawo kafin ya zama mai gyaran takalmi. Bayanai sun ce dangin Umuidenyi a Aji suna bikin ranar su, saboda haka, mahaifiyar Johnson ta bar mijinta da danta a gida su kadai don halartar taron wanda ya gudana a dakin taro na Umuidenyi. An ce Johnson ya sadu da mahaifinsa a cikin gida kuma ya yi amfani...
Gwamnan Jihar Enugu Ifeanyi Ugwuanyi ya bayar da umarnin sake gina wasu masallatai biyu da aka lalata a jihar

Gwamnan Jihar Enugu Ifeanyi Ugwuanyi ya bayar da umarnin sake gina wasu masallatai biyu da aka lalata a jihar

Crime
Gwamnan Jihar Enugu Ifeanyi Ugwuanyi ya bayar da umarnin sake gina wasu masallatai biyu da aka lalata a jihar yayin hatsaniyar da ta faru a satin da ya wuce. Masu zanga-zangar sun lalata masallatan ne a yankin Nsukka na jihar dake a kudu maso gabashin kasar. Shugaban karamar hukumar Nsukka Mista Cosmas Ugwueze ne ya bayyana hakan yayin ziyarar da ya kai masallatan da abin ya shafa a madadin gwamnan jihar.  
Gwamnan Enugu ya Roki Jami’an tsaro da su koma bakin aiki A Jihar

Gwamnan Enugu ya Roki Jami’an tsaro da su koma bakin aiki A Jihar

Tsaro
Gwamnnan jihar Enugu Ifeanyi Ugwuanyi a ranar Laraba yayi kira da Jami'an tsaro da sy koma bakin aikin su a fadin jihar. Gwamann ya yi wannan kiran ne, a yayin da ya kai wata ziyara izuwa ofishin kwamishinan 'yan sandan jihar domin jajanta masa kan asarar wasu jami'ai da rundunar tai tare da raunata wasu a sakamakon zanga-zangar adawa da rundunar SARS da ya faru a makwanin da su ka gabata. A cewar sa, Gwamnatin jihar ta kafa kwamiti da zai duba yawan barnar da ta afku tare da tallafawa wadanda lamarin ya rutsa dasu. Da ya ke jawabin maraba Kwamishinan 'yan sandan jihar CP Ahmad Abdurrahman godewa gwamnann yayi bisa ziyarar da ya kawo wa rundunar.
Sanata Shehu Sani yayi Allah wadai da kona Masallaci a Enugu

Sanata Shehu Sani yayi Allah wadai da kona Masallaci a Enugu

Siyasa
Sanata Shehu Sani yayi magana akan harin da aka kaiwa Musulmai da kona masallaci a Nsukka dake jihar Enugu.   Sanata Sani yayi maganane ta shafinsa na sada zumunta inda yace lamarin abin Allah wadai ne.   Yayi kiran da a dauki matakin doka akan wanda suka yi wannan aiki da kuma sake gina masallacin da aka kona.   The reported attack on the Muslim community and the burning of a mosque in Nsukka Local Government of Enugu State Stands unreservedly condemned.The State Government must ensure that the perpetrators of such heinous act be brought to book & the Mosque urgently rebuilt. https://twitter.com/ShehuSani/status/1323265274116800512?s=19
Shugaba Buhari da Atiku Abubakar sun yi jimamin Rasuwar mutane 21 a Hadarin Motar Enugu

Shugaba Buhari da Atiku Abubakar sun yi jimamin Rasuwar mutane 21 a Hadarin Motar Enugu

Siyasa
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya nuna Alhinin rasuwar mutane 21 da hadari ya rutsa dasu a karamar hukumar Awgu dake jihar Enugu.   Hadarin wanda yawanci yara ne 'yan makaranta ya rutsa dasu ya farune a ranar Laraba. Kakakin shugaban kasar, Femi Adesina ya bayyana cewa shugaba Buhari yayi fatan Allah ya baiwa iyalan mamatan hakuri. Hakanam shima tsohon mataimakin shugaban kasa,  Atiku Abubakar a sakon ta'aziyyar nasa inda yace lamarin akwai sosa zuciya sosai.   Ya mika sakon ta'aziyya ga iyalai, Malamai dama makarantar mamatan inda ya musu fatan Samun Rahama.   The gruesome accident in Mgbowo, Awgu Local Government Area of Enugu State, in which scores of lives, many of them school children were lost is heartbreaking.   My deepest condolen...
Mutane 21 sun mutu yayin da motar makaranta da tirela suka yi karo a Enugu

Mutane 21 sun mutu yayin da motar makaranta da tirela suka yi karo a Enugu

Uncategorized
Hukumar kiyaye haddura ta kasa, a ranar Alhamis, ta tabbatar da mutuwar mutane 21, ciki har da yara ‘yan makaranta, a wani hatsarin mota a Mgbowo da ke karamar hukumar Awgu ta jihar Enugu. Kwamandan sashen na Enugu, Mista Ogbonna Kalu, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ga jaridar The PUNCH, ta wayar tarho, ya ce hatsarin ya afku ne da yammacin ranar Laraba. Ya ce hatsarin ya rutsa da motar makaranta da tirela. Kwamandan ya dora alhakin hatsarin kan saurin wuce gona da iri da tuki mai hatsari. Kalu ya ce, “An tabbatar da mutuwar mutane 21 kuma sama da mutane 50 na cikin motar makarantar. “Har ila yau, abin lura shi ne, ba duk wanda suka mutu a motar yan makarantar ba ne. Wadanda ke aiki a gefen hanya na daga cikin wadanda suka mutu. "Daga bayanan da ke akwai, hatsarin y...
Rundunar ‘Yan Sanda reshan Jihar Enugu Sun Cafke Wasu Mutane 23 da ake zargi da hannu a zanga-zangar SARS

Rundunar ‘Yan Sanda reshan Jihar Enugu Sun Cafke Wasu Mutane 23 da ake zargi da hannu a zanga-zangar SARS

Tsaro
Rundunar ‘yan sanda ta jihar Enugu ta cafke mutane 23 da ake zargi da hannu a zanga-zangar SARS wanda ya rikide ya zama rikici a cikin jihar sakamakon haka ya haifar da kashe-kashe da lalata dukiyoyin jama'a. Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ahmad AbdurRahman ne ya bayyana hakan a yayin da ya ke gabatar da wadanda ake zargin a Enugu ranar Laraba. AbdurRahman ya ce rundunar ta kama wadanda ake zargin ne bisa laifuka daban-daban wanda a cewarsa laifukan sun hada da "laifukan makirci, yin taro ba bisa ka'ida ba da tayar da tarzoma, kisan kai, kone-konen mummunar barna, sata, toshe hanyoyi, tunzura jama'a tare da haifar da rabuwar kai. Rundunar ta gargadi matasa da su kasance masu bin doka da oda don kaucewa fadawa hannun hukuma.
Biliyan 10 gwamnati ta kashe wajan gyaran Filin jirgin Sama na Enugu>>Hadi Sirika

Biliyan 10 gwamnati ta kashe wajan gyaran Filin jirgin Sama na Enugu>>Hadi Sirika

Siyasa
Gaamnatin tarayya ta bayyana cewa ta kashe Biliyan 10 wajan gyaran Filin jirgin sama na Akanu Ibiam dake jihar Enugu.   Ministan Sufurin jiragen sama,  Hadi Sirika ne ya bayyana haka a yayin kaddamar da aikin a jiya Lahadi.  Hutudole ya fahimci Hadi Sirika yace lura da yanda Filin jirgin saman ke da muhimmanci wajan ayyukan tattalin arzikin yankinne yasa ya kaiwa shugaba Buhari bukatar gyarashi. Yace kuma shugaban ya amince a yi gyaran akan Biliyan 10. Ya kara da cewa jiragen saman Najeriya a yanzu zasu iya fara aiki da Filin jirgin kuma nan da 5 ga watan Satumba .