fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

Tag: Fashi

Mutane 2 sun mutu, an harbi dan sanda a fashin hanyar Kogi

Mutane 2 sun mutu, an harbi dan sanda a fashin hanyar Kogi

Tsaro
Lamarin ya farune da misalin karfe 6 na yammacin jiya, Lahadi a daidai Osara, tsakanin Itakpa da Kabba inda 'yan fashi suka bude wuta.   Rahotanni sun bayyana cewa 'yan Fashin sun kashe mutum 2 tare kuma da harbin wasu ciki hadda dan sanda. Wanda suka mutu din 'yan asalin Kogi ne dake zaune a jihar Katsina, kuma sun dawo daga ganin gidane yayin da lamarin ya faru.   Wata mata data tsallake harin ta shaidawa Punch cewa, harin ya saka fargaba azukatan mutane kuma da dama sun shiga halin kaka nikayi inda aka tara motoci da yawa akan hanya.   Saidai 'yansandan jihar sunce basu da masaniya akan wannan hari.
Dan fashi ya dirkawa abokin fashinshi harsashi

Dan fashi ya dirkawa abokin fashinshi harsashi

Tsaro
Wani dan fashi daga jihar Ondo ya bindige abokin fashinshi yayin da suke kan hanyar tserewa bayan kwacewa wata mata dake shagon OPS Dubu 60.   Lamarin ya farune a yankin Okitipupa inda bayan sun yi fashin suna neman tserewa sai matar da suka sacewa kudin ta kurma Ihu. Jama'a sun rufarwa 'yan fashin, da daya daga ciki yaga ana neman kamasu sai yayi harbi a iska, garin hakane ya bindige abokin aikin nasa. 'Yansanda sun dira wajan da lamarin ya faru inda suka dauke gawar Wanda ya mutu da aka bayyana sunanshi da Kehinde inda suka samu kudin da aka yi fashin da kuma bindiga.   Sun tabbatar da cewa nan ba da dadewa ba za'a kamo wanda suka tsere.
Wasu mutane a jihar Ekiti sun kashe kafinta da aka yi kuskuren cewa dan fashi da makami ne

Wasu mutane a jihar Ekiti sun kashe kafinta da aka yi kuskuren cewa dan fashi da makami ne

Uncategorized
Wani kafinta dan shekaru 45, Olufalayi Obadare, ya rasa ranshi a hannun wasu mutane dake zargin cewa shi dan fashi ne a yankin Olujoda da ke Ado Ekiti, babban birnin jihar Ekiti.   An samu rahoto cewa wasu matasa, wadanda suka hango kafinta yana yawo a unguwar da misalin karfe 5 na yamma a ranar Talata, sun kuskure shi a matsayin daya daga cikin yan fashin da ke damun yankin. An bayar da rahoton cewa matasan sun haumasa da muggan makamai wanda hakan yayi sanadiyyar mutuwar shi. Matar Obadare, Yemi, wacce ta ce mijinta, mahaifin yara uku, ya bar gidansu ranar Talata don zuwa yankin Olujoda don ganawa da wani abokin cinikinsa, ta ce cewa sam ba daidai ba ne matasan su kuskure shi a dan fashi ba tare da tabbatar da zargin na su ba. Matar  ta bukace yan sanda da...
Yan fashi sun shiga gidan alkali, sun saci dala 1,000 da wasu abubuwa

Yan fashi sun shiga gidan alkali, sun saci dala 1,000 da wasu abubuwa

Tsaro
Yan sanda a ranar talata sun gurfanar da wasu mutane biyu da ake zargi da fashi da makami, wadanda a ranar 22 ga Fabrairu, 2020, suka shiga gidan Ikoyi, wani alkalin Legas, da suka kwace dala 1,000, nera 250,000, agogon hannu hudu, talabijin mai nauyin inci 50, da riguna biyu da takalma biyu. Wadanda ake tuhumar, Friday Eze da Anuoluwa Adeware - tare da wadanda suka taimaka masu, Rasaq Bolaji da Beatrice Elom, an gurfanar dasu gaban kuliya akan tuhuma guda 15 a babbar kotun tarayya da ke Legas. Dangane da tuhumar da yan sanda suke yi masa, Eze da Adewale, tare da wani Monday Uvi da sauran wanda da ba'a san inda suke  ba har yanzu, sun mamaye gidan alkalin dauke da bindiga, adda da wasu makaman, inda suka kwace masa kadarorin shi. Masu gabatar da kara sun ce wadanda ake kara su...