fbpx
Friday, March 31
Shadow

Tag: Gen Yakubu Gowon

Gowon ya karyata ikirarin Majalisar Dokokin Burtaniya cewa ya ‘saci rabin kudin Babban Bankin Najeriya zuwa Ingila

Gowon ya karyata ikirarin Majalisar Dokokin Burtaniya cewa ya ‘saci rabin kudin Babban Bankin Najeriya zuwa Ingila

Siyasa
Tsohon shugaban kasar Najeriya, Yakubu Gowon, ya musanta zargin da ake yi masa cewa ya kai “rabin kudaden Babban Bankin Najeriya kasar ingila”. Wani dan majalisar dokokin Burtaniya, Tom Tugendhat, ne ya yi wannan ikirarin yayin muhawara kan harbe-harbe da akayi Lekki ga masu zanga-zanga. Tugendhat ya ce "mun san cewa a yau, ko da a yanzu, a cikin wannan babban birni namu, akwai, abin bakin ciki, wasu mutane da suka karɓa daga mutanen Najeriya suka ɓoye ribar da suka samu a nan." Ya ce Gowon yana daya daga cikinsu. A cewarsa, Gowon ya dauki rabin CBN zuwa Ingila. Sai dai kuma, a wata hira da BBC, Gowon ya bayyana zargin a matsayin "karya". Ya ce: “Abin da dan majalisar ya fada karya ne. Ban san daga ina ya samo wannan shara ba. Na yi wa Najeriya aiki tukuru kuma bayanan ...
Bidiyon Yanda Tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon ya kwashi rabin kudin CBN zuwa kasar Ingila>>Majalisar Ingila

Bidiyon Yanda Tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon ya kwashi rabin kudin CBN zuwa kasar Ingila>>Majalisar Ingila

Siyasa
Majalisar Kasar Ingila ta yi zama akan bukatar sakawa Najeriya takunkumi saboda zargin harbe-harben da aka yi a Lekki Toll Gate yayin zanga-zangar SARS.   Gwamnatin tarayya ta karyata cewa an rasa rayuka a wajan inda tace Bidiyon karyane kawai aka rika yadawa a shafukan sada Zumunta.   Wani dan majalisar kasar ta Ingila ya bayyana bukatar cewa ya kamata a dakatar da masu satar kudin Najeriya suna kaiwa kasar ta Ingila suna boyewa.   A wani Bidiyo da ya watsu sosai a shafukan sada zumunta, an ji dan majalisar na bada Misali da yanda tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon ya kwashi rabin kudin babban bankin Najeriya,  CBN ya tafi dasu kasar ta Ingila.   https://twitter.com/LifeOfChika/status/1330960530643644416?s=19
Buhari na bukatar Addu’a>>Tsohon Shugaban kasa, Yakubu Gowon

Buhari na bukatar Addu’a>>Tsohon Shugaban kasa, Yakubu Gowon

Siyasa
Tsohon shugaban Najeriya, Janar Yakubu Gowon ya bukaci 'yan Najeriya Kiristoci su saka shugaban kasa, Muhammadu Buhari a addu'a,  ya bayyana cewa shugaban na bukatar addu'a saboda kada Najeriya ta ruguje a hannunshi.   Gowon ya bayana hakane ta bakin Ministan ayyuka na musamman, George Akume wanda ya wakilceshi wajan nada sabon sakataren hukumar aikin Ibadar Kiristoci. Yace yasan shugaban kasa, Muhammadu Buhari na iya bakin kokarinsa amma har yanzu akwai matsaloli a kasarnan, yace amma ta hanyar yin addu'a,  za'a shawo kan matsalar.
Nnamdi Kanu: Ya yiwa Gowon, Olusegun Obasanjo martani kan kalaman da suka yi ga Inyamurai

Nnamdi Kanu: Ya yiwa Gowon, Olusegun Obasanjo martani kan kalaman da suka yi ga Inyamurai

Siyasa
Nnamdi Kanu, shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra(IPOB) ya yiwa tsohon Shugaban Kasa, Janar Yakubu Gowon, tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo da kuma tsohon hafsan soji, Janar Theophilus Danjuma, ihu bisa ga kiran da suke yi na sake fasalin kasar.   Janar Yakubu Gowon (retd), wanda ya halarci wani taro wanda Gidauniyar Shugabanci ta Igbo ta shirya a ranar Alhamis, ya yarda cewa an bar ƙabilar Igbo a baya a siyasar Nijeriya.   Ya ce, "Na yi imani da cewa an yi wa Igbo rashin dai dai, batun tsarin mulki ya kama a magance shi tare da samun daidai to, da kuma dawo da kwarin gwiwa ga kowa.   Haka Shima Obasanjo ya yi Allah wadai da halin da ake ciki a kasar nan a cikin jawabin da ya yi a ranar Asabar a bikin gabatarwa na tunawa da Frederick Fase...