
Na godewa wanda ya fara tattaki daga Kaduna zuwa Zamfara dan ya gaisheni amma ina bashi shawarar ya koma gida ya yi abinda zai amfaneshi>>Gwamnan Bello
A bayane muka ji labarin yanda wani Matashi ya taso daga garin Giwa dake Kaduna da niyyar zuwa Zamfara dan gaishe da masoyinsa, Gwamnan jihar, Dr. Bello Matawalle.
Saidai a matartanin Gwamnan ta shafinsa na sada zumunta ya godewa matashin inda yace yana bashi shawarar ya koma gida yayi abinda zai amfani rayuwarsa.
https://twitter.com/Bellomatawalle1/status/1309597105292537856?s=19
Yace a matsayinsa na Uba ya na kira ga matasa su daina irin wannan tafiya me hadari.
Wani matashi, Masoyin shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne ya fara yin wannan tattaki inda yaje Abuja dan taya shugaban kasar Murnar lashe zabe a shekarar 2015.