fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Tag: Giya

Wani Lauya ya maka Jihohin Jigawa, Kano da sauransu a Kotu inda yace tunda dai sun haramta shan Giya to su dawo da Harajin giya da suka karba

Wani Lauya ya maka Jihohin Jigawa, Kano da sauransu a Kotu inda yace tunda dai sun haramta shan Giya to su dawo da Harajin giya da suka karba

Siyasa
Wani lauya, Sesugh Akume ya maka jihohin da suka haramta shan giya a Najeriya a kotu inda yace yana neman su dawo da kudin harajin giya da aka basu.   Ya saka babban lauya na gwamnatin Tarayya da Hukumar EFCC a cikin wanda yake kara.   Yace wadannan jihohi suna karbar kudi daga gwamnatin tarayya wanda kuma akwai harajin giya a cikinsu. Yace amma kuma sai su rika hana kasuwancin giya da caca suna lalatasu.   Yace misali A Kano, Hisbah na irin wannan abu da kuma Jihar Jigawa. Yace yana so a hanasu saboda kundin tsarin mulkin Najeriya da ba ruwansa da Addini bai haramta ta'ammuli da Giya ba.   Jihohin Arewa da suka haramta ta'ammuli da giya sun hada da Kano, Kaduna, Katsina, Kebbi, Sokoto, Borno, Yobe, Jigawa, Bauchi, Gombe, Zamfara da Niger. &nb...
A jihar Kaduna ma Hisbah ta lalata giya

A jihar Kaduna ma Hisbah ta lalata giya

Siyasa
Kwanaki kadan bayan da Hisbah a jihar Kano ta lalata giya ta miliyoyin Naira, a jihar Kaduna ma, Hisbah ta lalata giya.   Lalata giyar da Hisbah ta yi a jihar Kano ya jawo cece-kuce sosai musamman daga mutanen kudancin Najeriya. Just like in Kano state, Hisbah officials have destroyed a beer parlour and crates of beer in Sabon Gari area of Kaduna state. Recall that over the weekend, Hisbah operates destroyed beer worth N200 million in Kano.
Dan shekaru 11 ya mutu a wajan gasar Shan Giya bayan da ya sha kwalba 5

Dan shekaru 11 ya mutu a wajan gasar Shan Giya bayan da ya sha kwalba 5

Uncategorized
Lamarin ya farune a kasar Malawi, inda yaron dake aji 7 na makarantar Firamare dan shekaru 11, Humphrey Chipeta ya shiga gasar.   Ya kai zagaye na karshe na gasar inda ya kwankwadi giya kwalba 5 kuma daga nan sai ya mutu. Saidai wani shaida, Emmanuel Chirwa ya bayyana cewa akwai wata makarkashiya a mutuwar yaron dan kuwa shine ma ya lashe gasar da aka yi ta baya. Ana saka Dubu 20 kudin kasar Malawin ga duk wanda ya lashe gasar.   Lamarin ya farine a yankin Mzimba na kasar inda kuma tuni kungiyoyin kare hakkin yara suka ce zasu shiga maganar, Musamman lura da cewa ba Humphrey ne kadai yaro a cikin gasar ba.
Tunda dai ‘yan Arewa sun ce basu shan giya ya kamata a hanasu karbar haraji a kanta>>Dan Majalisa

Tunda dai ‘yan Arewa sun ce basu shan giya ya kamata a hanasu karbar haraji a kanta>>Dan Majalisa

Siyasa
Dan majalisa daga jihar Rivers, Awaji Inombek Abiante ya bayyana cewa yana goyon bayan a rika raba kudin shigar da ake samu daga jihohin Najeriya inda jihar da ta samar da kudin zata dauki rabi, gwamnatin tarayya ma ta dauki rabi.   Tun a bayane ya gabatar da wannan kudiri a majalisar Wakilai wanda kuma ya kai matakin karatu na 2 amma daga baya aka ki amincewa dashi. Saidai a hirar da yayi da Punch ya bayyana cewa yana nan kan batunsa. Hutudole ya fahimci maganar da Dan majalisar yayi akan karbar harajin kudin Giya. Yace jihohin Arewa da basa shan giya ya kamata a hanasu karbar haraji akanta.   Yace abar masu zuwa suna sha suna tambele wasu ma har su yi tuki su yi hadari su rika amfana da harajin amma kai kace baka sha kuma kana karbar haraji akanta, wannan ba ...
Hisbah ta lalata kwalaben giya 588 a Jigawa

Hisbah ta lalata kwalaben giya 588 a Jigawa

Uncategorized
Hukukar Hisbah a jihar Jigawa ta lalata kwalaben giya 588 a rabar 20 ga watan Augustannan da muke ciki.   Shugaban Hisbah na jihar, Ibrahim Dahiru ne ya tabbatar da haka ga manema labarai inda yace sun kama giyar ne a kauyukan Tudun Baye dake karamar hukumar Ringim dake jihar. Dahiru ya bayyanawa kamfanin dillancin labaran Najeriya, NAN cewa an haramta shan giya a jihar kuma ba zasu taba bari ana ta'ammuli da ita ba da sauran ayyukan assha.
Hisbah ta kama adaidaita Sahu cike da giya a Kano, direban ya tsere

Hisbah ta kama adaidaita Sahu cike da giya a Kano, direban ya tsere

Siyasa
Hukuma Hisbah a Kani ta kama wani Adaidaita Sahu dake kokarin yin fasa kwaurin giya zuwa cikin jihar.   Saidai Direban ya tsere. Kwamandan Hisbah, Haruna Muhammad Sani Ibn Sina ya tabbatar da haka bayan kamen da aka yi a karshen makonnan. Yayi kira ga masu adaidaita su daina yadda ana amfani dasu ana shigar da haramtattun abubuwa cikin jihar. Ya kuma kara da cewa mutane a jihar su ci gaba da bada hadin kai wajan tona ayyukan ashsha.