
Asusun Bada Tallafin Duniya Na Global Fund, Ya Tallafawa Najeriya Da Dala Miliyan 890 Don Yaki da Cututtuka
Asusun bada tallafi na duniya ‘Global Fund’ ta tallafa wa gwamnatin Najeriya da dala miliyan 890 domin yaki da cututtuka a kasar.
Wadannan cututtuka sun hada da cutar kanjamau, zazzabin cizon sauro da tarin fuka.
Ministan kiwon lafiya Osagie Ehanire ya Sanar da haka a makon da ya gabata a Abuja.
Ehanire ya ce samun wannan tallafi zai taimaka wajen inganta fannin kiwon lafiyar kasar nan musamman bangaren yaki da wadannan cututtuka da suka yi wa kasar nan katutu.
Idan ba a manta ba a watan Janairu 2020 Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa za ta ciwo bashin dala miliyan 890 daga asusun duniya domin dakile yaduwar cututtuka a kasar nan.
Gwamnati ta ce za ta kashe wadannan kudade wajen yaki da cutar Kanjamau, Zazzabin Cizon Sauro da tarin fuka daga shekarar 2021 zuwa...