
“Ku zabi PDP don ta ceto Najeriya daga mawuyacin halin datake ciki”>> Tambuwal
Gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal mai neman takarar shugabanci a jam'iyyar PDP, yayi kira ga al'ummar Najeriya cewa su zabi PDP domin ta ceto kasar a mawuyacin hali data ciki.
Tambuwal ya fadi hakan ne a gidan sakateriyar PDP dake jihar Kaduna a ranar asabar, inda ya gudanar da taro tare da membobin jam'iyyar.
Tsohon gwamnan Sokoto Bafarawa ya halacci taron dare sauran manyan jam'iyyar PDP, kuma Tambuwal ya kara da cewa jihar Kadune ta PDP ce domin sunada kansiloli bila adadin a jihar.