fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Tag: Hadarin Mota

Hadarin Mota Yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 2 A Jihar Kano

Hadarin Mota Yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 2 A Jihar Kano

Uncategorized
Kusan kwana uku bayan da mutane hudu suka rasa rayukansu a cikin Kano, wasu mutane biyu sun mutu a ranar Laraba lokacin da motoci uku sukayi taho mugama a Titin Panshekara a cikin birnin.   A cewar kakakin Hukumar Kula da Haddura ta Tarayya a jihar, Kabir Daura, hadarin ya faru ne a kan layin Panshekara na babbar hanyar mota. A cewarsa, hadarin ya shafi wata motar dauke da dabbobi, Toyota Space Wagon da babur mai kafa uku, wanda aka ce matukin ta yana tukin gan ganci a gaban motar. Daura ya ce, "A kokarin kaucewa wannan babur din, direban motar ya kutsa cikin wata mota da babur din, ya ja su zuwa shagon da ke gefan titin, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane biyu, wani dattijo da kuma wata yarinya mace." Jim kadan bayan hadarin, ya ce jami'an hukumar FRSC sun kwas...
Mutane Uku Sun Mutu, Shida Sun Ji Rauni Yayin Da Wata Bas Ta Wunstila a Jihar Ogun

Mutane Uku Sun Mutu, Shida Sun Ji Rauni Yayin Da Wata Bas Ta Wunstila a Jihar Ogun

Uncategorized
An ce wata yarinya 'yar shekara shida da wata mace sun mutu a wani mummunan hadarin da ya afku a kan babbar hanyar Legas zuwa Sagamu. An bada rahoton cewa wasu fasinjoji shida sun sami raunuka daban-daban a hadarin. Kakakin Hukumar Kula da zirga-zirgar  Jihar Ogun, Babatunde Akinbiyi, ya tabbatar da faruwar lamarin. Akinbiyi ya ce, hadarin ya faru ne da misalin karfe 2:05 na daren ranar Talata a sansanin Matasa, Inbound Legas. Ya kunshi mota kirar Mazda tare da lambar rajista, FUF 109 ZD. An tattaro cewa tayar bas din ta fashe yayin da take tafiya kuma sai ta wuntsila. "A cewar shaidun gani da ido, an samu labarin cewa motar bas din tana zuwa ne daga jihar Kwara zuwa cikin jihar Legas, lokacin da tayar ta ta fashe saboda tsananin gudu" wanda yayi sanadiyyar mu...
Hadarin mota ya ci rayuka 3 a Katsina

Hadarin mota ya ci rayuka 3 a Katsina

Uncategorized
Rahotanni daga jihar Katsina na cewa hadarin mota yaci rayuka 3 da jikkata mutane 9 a hanyar Batsari zuwa Katsina.   Lamarin ya farune da misalin karfe 9 na dare a kan hanyar Bakiyawa, kamar yanda wasu ganau suka shaidawa majiyarmu. Wani me karamar mota Honda ne yayi kokarin wuce wani adaidaita Sahu da babu saidai motar ta kwace masa ya auka musu.   Kwamandan hukumar kula da hadaruka na jihar, Ali Tanimu ya tabbatar da faruwar lamarin.
Mutane 4 sun mutu a hadarin mota a Bauchi

Mutane 4 sun mutu a hadarin mota a Bauchi

Siyasa
Wani hadarin mota da ya rutsa da mutane a hanyar Toro dake tsakanin Jos da Bauchi da yammacin jiya, Juma'a yayi sanadin kisan mutane 4.   Lamarin ya farune yayin da ake ruwan sama kamar da bakin kwarya, Motocin Opel Vectra 2 suka yi karo da juna ta gaba. Yawancin wanda suka rasu dai 'yan kasuwane dake sayar da kaya a cikin Bauchi, kamar yanda muka samo.
Bidiyo:Yanda ‘yansandan Najeriya suka harbi mota saboda takunkumin rufe baki da hanci, ta yi hadari mutane 3 suka mutu

Bidiyo:Yanda ‘yansandan Najeriya suka harbi mota saboda takunkumin rufe baki da hanci, ta yi hadari mutane 3 suka mutu

Uncategorized
Wannan wani Bidiyo ne daya dauki hankula a shafukan sada zumunta inda aka ga wata farar Mota da ta yi hadari.   A bayanan da ake ji a cikin Bidiyon, Shaidun gani da ido sun ce an harbi tayar motarne saboda takunkumin rufe baki da hanci wanda kuma sanadin haka ta yi hadari mutane 3 suka mutu.   Lamarin ya farune a garin Warri na Jihar Delta kamar yanda hutudole ya fahimta.   Kalli bidiyon a kasa:
Mutum 7 ‘yan gida daya da ke tafiya don jana’iza sun mutu a hadarin mota

Mutum 7 ‘yan gida daya da ke tafiya don jana’iza sun mutu a hadarin mota

Uncategorized
Mutane bakwai da ke tafiya don jana’izar mamaci sun mutu a wani hatsarin mota da ya afku a kan titin Ogidi-Abatete a karamar hukumar Idemili ta jihar Anambra. Wasu mutane da dama dake tafiya tare da mamatan sun samu raunika dayawa. Hadarin, wanda ya faru da misalin karfe 5.15 na daren ranar Juma'a, ya shafi wata motar daukar yashi da kuma wata motar bas dauke da mutane 19. An ce bas din na dauke da iyale ne wanda ke hanyar zuwa bikin binne yan uwansu alokacin da suka hade da motar daukan yashin. Wani shaidar gani da ido ya ce, “Mutane  bakwai ne suka mutu a wannan wurin yayin da wasu fasinjoji suka samu raunuka. "Yawancinsu yan gida daya ne wanda ke hanyar zuwa wurin jana'izar." Jami’in sashen kula da lamuran jama’a na hukumar kula da lafiya ta kan titi na tar...
Dalibar jami’ar Bayero Ta rasu Sanadin Hadarin Mota a Kano

Dalibar jami’ar Bayero Ta rasu Sanadin Hadarin Mota a Kano

Uncategorized
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Wannan Baiwar Allah Mai Suna Maryam H. Umar Ta Rasu Sakamakon Hadarin Mota A Kano     Kafin rasuwarta daliba ce a jami'ar Bayero, inda take mataki na 400 a fannin harkar magunguna. An yabe ta cewa mutuniyar kirki ce, sannan ko a lokacin da za ta rasu babu abinda ke fita daga bakin ta sai kalmar shahada.     Allah ya gafarta mata. Ya kuma baiwa 'yan uwanta hakurin jure rashinta. Rariya.
Hadarin Mota yayi sanadin Rasa rayuka 5 a Kano

Hadarin Mota yayi sanadin Rasa rayuka 5 a Kano

Uncategorized
Wani mummunan hadarin mota daya faru a Rimin Gata, dake Karamar Hukumar Ungoggo a Kano yayi sanadin mutuwar mutane 5.   Hadarin ya farune tsakanin motar Tifa da Motar Golf dake dauke da mutane 10.   Me magana da yawun hukumar kula da Gobara ta jihar, Saidu Muhammad na cikin wanda suka yi aikin tseratar da wanda suka rayu.   Ya bayyana cewa sun fitar da mutane 5 da rai yayin da 5 kuma sun rigamu gidan gaskiya.
Mutane Bakwai Masu Zuwa Wa’azin Izala Daga Jihar Neja Zuwa Abuja Sun Rasu Sakamakon Hadarin Mota

Mutane Bakwai Masu Zuwa Wa’azin Izala Daga Jihar Neja Zuwa Abuja Sun Rasu Sakamakon Hadarin Mota

Uncategorized
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Ayarin matafiya wa'azin ƙasa da ƙungiyar Jama'atul Izalatul Bidi'a Wa'iƙamatus Sunnah (Nat. HQT Jos) za ta gudanar a babban birnin tarayya Abuja sunyi hadari a jihar Neja, inda mutane bakwai suka riga mu gidan gaskiya yayin da mutane huɗu suka samu mummunar raunuka waɗanda ake cigaba da duba lafiyar su a babban asibitin Aminu Goje dake garin Bangi.   Matafiyan waɗanda suka taso daga garin Bangi dake Jihar ta Neja sunyi hatsarin ne a tsakanin garin Galma zuwa Igwama dake ƙaramar hukumar Mariga a yau asabar, inda rahotanni suka tabbatar da wani mai ƙaramar motane ya gitta masu yayin da suke tsakar tafiya wanda hakan yasa motar ta ƙwacewa direbar suka nufi daji.   Tuni aka yiwa mamatan jana'iza a garin Bangi kamar yadda addinin musu...