fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

Tag: Hisba kano

Hisbah ta kama mabarata 178 a jihar Kano

Hisbah ta kama mabarata 178 a jihar Kano

Siyasa
Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta cafke wasu mutane 178 da ake zargi a cikin garin Kano saboda karya dokar hana bara a kan titi daga Satumba zuwa Nuwamba 2020. Babban kwamandan hukumar, Mista Haroun Ibn-Sina, ne ya fadi hakan a Kano ranar Litinin. “An cafke wadanda ake zargin ne a hanyar Alu Avenue, Dan’agundi, Taludu, Race Course, Sharada, Kofar Mazugal a cikin garin. “Daga cikin wadanda aka kama 102 mata ne, yayin da 76 maza. “Hukumar za ta ci gaba da cafke mabaratan da suka ki bin doka.
Hukumar Hisbah ta kama karuwai 32, 12 daga ciki an tabbatar da suna ɗauke da ƙwayar cutar Kanjamau

Hukumar Hisbah ta kama karuwai 32, 12 daga ciki an tabbatar da suna ɗauke da ƙwayar cutar Kanjamau

Crime
Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta cafke wasu karuwai har guda 32 wadanda 12 daga ciki aka tabbatar sa suna dauke da cutar kanjamau. Kwamandan Hisba na jihar Muhammad Harun Ibn Sina shine ya bayyana hakan ga manema labarai a jihar kano. Muhammad Harun ya bayyana cewa, an kama karuwanne a wani sumame da hukumar ta kai a wata kusuwa dake Badume a karamar hukumar Bichi. A cewarsa, kamen wanda hadin gwaiwa ne da hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa reshan jihar kano. Ya kara da cewa a yayin sumamen, jami'an hukumar sun kama wata mata da ta kware a harkar sayar da kwaroron roba da kuma wasu maza tara da ke sayar da kwayoyi. Hakanan kwamanda ya shaida cewa, karuwan da hukumomin suka cafke galibin su sun fito ne daga jihohin Edo, Anambra, Adamawa, Enugu, Zamfara, Kats...
Hukumar Hisba ta Jihar Kano ta horar da Jami’anta Dabarun kare kai

Hukumar Hisba ta Jihar Kano ta horar da Jami’anta Dabarun kare kai

Tsaro
Kungiyar Karate ta jihar kano ta baiwa Jami'an hukumar Hisba 200 horo na dabarun kare kai daga abokan gaba. An bayyana hakan ne a wata sanarwa da Kakakin Hukumar Lawal Ibrahim-Fagge ya fitar a ranar Alhamis. Kwamandan hukumar Hisba ta jihar Kano Harun Ibn sina, ya matukar yabawa da horon da a ka baiwa Jami'an sa, ya kuma Kara da cewa daman horon ya zama wajubi ga Jami'an kasancewar su ba makami su ke rikewa ba. Haka zalika kwamandan Ya kara da cewa "irin wannan horon zai taimaka musu wajen kare kansu idan an kai musu hari. Horan da kungiyar ta baiwa Jami'an ya hada da gudun tsere, dabarun kare kai gami da yadda mutum guda zai iya tunkarar mutane uku shi kadai. Hakanan an kuma koyawa Jami'an yadda a ke fasa Bulo da hannu, tare da sauran wasu dabaru.