fbpx
Tuesday, March 28
Shadow

Tag: Idi

Jihar Naija ta tsige Limamai 3 daga matsayinsu saboda Jagorantar Sallar Idi

Jihar Naija ta tsige Limamai 3 daga matsayinsu saboda Jagorantar Sallar Idi

Siyasa
Gwamnatin jihar Naija ta bayyana tsige limamai 3 daga matsayinsu na limanci saboda jagorantar Sallar Idi wanda hakan ya sabawa dokar da gwamnatin jihar ta saka na hana Sallar Juma'i dan dakile yaduwar cutar Coronavirus/COVID-19.   Daraktan harkokin Addini na jihar, Dr. Umar Farouq Abdullahi ne ya bayyana haka ga manema labarai inda yace an cire malam Abdullahi Ndakogi na garin Batagi saboda jagorantar Sallar Idi a garin.   Me magana da yawu  Daraktan, Mustapha Tauheed ne ya bayyana haka inda yace an maye malam Abdullahi Ndakogi da wani limamin.   Shima dai wani Malam Muhammad Idris dake Rukunin gidajen Bosso an tsigeshi inda aka ce na'ibinsa ya karbi aikin limanci, an kama malam Idris ne da laifin jagorantar sallar Taraweeh data Tahajjud lokacin Azumin wata...
Ku Gudanar Da Gajeriya Huduba A Sallar Idin Bana>>Gwamna Ganduje Ga Malamai

Ku Gudanar Da Gajeriya Huduba A Sallar Idin Bana>>Gwamna Ganduje Ga Malamai

Uncategorized
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya shawarci malaman addini a Kano da su gabatar da gajeriyar huduba yayin sallar idi.     A wata takarda da sakataren yada labaran gwamnatin jihar, Abba Anwar ya fitar a jiya, ya ce za a yi sallar idi a kananan hukumomi 44 da ke fadin jihar. Amma dole ne Musulmai su kiyaye dokokin da hukumomin lafiya suka tanadar don sallar jam'i.   "Kamar yadda manyan Malamai suka shawarci limamanmu, ya kamata a yi huduba gajera a yayin sallar Idin saboda kalubalen Corona virus da muke fuskanta".     Ya ce akwai bukatar jama'a su hanzarta watsewa ana kammala sallar sannan su ci gaba da kiyaye dokokin kiwon lafiya.
Coronavirus/COVID-19 jarabawace daga Allah>>Atiku Abubakar

Coronavirus/COVID-19 jarabawace daga Allah>>Atiku Abubakar

Siyasa
Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP a zaben shekarar 2019, Alhaji Atiku Abubakar ya baygana cewa cutar Coronavirus/COVID-19 jarabawace daga Allah. A cikin sakon daya fitar na barka da Sallah ga 'yan Najeriya Atiku ya kuma jawo hankalin shuwagabanni da su fifita kula da jam'a a mulkinsu.   Ya bayyana cewa kare lafiyar mu data wanda ke tare samu na da muhimmanci dan haka ya jawo hankulan mutane da su bi dokar da hukumomi ke sakawa.   Yace an yi Azumi ba tare da Sauran ibadun da aka saba yi na sallar Asham ba da kuma cin abinci cikin jama'a da tafsir ba amma hakan bai sakawa Azuminmu rauni ba dan kuwa mun san cewa duk waji yanayi da muka tsinci kan mu a ciki daga Allah ne kuma dama Allah yayi Alkawarin gwada imanin mu. ...
‘Ana neman waɗanda suka ce sun ga wata’

‘Ana neman waɗanda suka ce sun ga wata’

Uncategorized
Kwamitin duba wata na Fadar Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ya ce yana neman agajin mutane da su taimaka masa wurin neman duk wanda ya ce ya ga watan Shawwal a daren Juma'a. Shugaban kwamitin, Farfesa Usman el-Nafaty ne ya tabbatar wa BBC hakan, inda ya ce suna neman mutanen ne domin tattaunawa da su da nufin tabbatar da sahihancin abin da suka gani. Tun farko wani shafin Facebook ne mai ɗauke da sunan kwamitin ganin watan ya wallafa sanarwar cewa ana neman mutanen. "Muna roƙo idan kuna cikin waɗanda suka ga watan Shawwal na shekarar 1441 a kowanne lungu da saƙo na Najeriya ranar Juma'a, ko kuma kun san wanda ya gani, ko kun san yadda za a cimma wanda ya gani to ku bayyana mana a nan," in ji sanarwar. Ta ƙara da cewa: "Mambobin kwamitin ganin wata na s...
Ina sane da halin matsin da kuke ciki, amma ku sani ba da gangan muka dauki matakai masu tsauri ba>>Shugaba Buhari

Ina sane da halin matsin da kuke ciki, amma ku sani ba da gangan muka dauki matakai masu tsauri ba>>Shugaba Buhari

Siyasa
Shugaban kasa,Muhammadu Buhari ya bukaci Musulmai su kasance cikin cikin karfin gwiwa duk da halin da Annobar cutar Coronavirus/COVID-19 ta zo dashi.   Shugaban nya bayyana hakane a cikin sakon barka da Sallah da ya aikewa 'yan Najeriya ta hannun me magana da yawunsa,Garba Shehu, kamar yanda ya bayyan a yau, Asabar. Shugaban yace ba abune me sauki ba yin azumi ba tare da Sallar Taraweeh ba da kuma Tafsir ba yace amma hakan ya zama dole saboda dakile yaduwar cutar Coronavirus/COVID-19.   Yace yana kira ga masu hali daga ciki su ci gaba da taimakawa wanda basu da shi dan a samu a gudu tare a tsira tare.   Yace yana yabawa da sadaukarwar da musulmai da Kiristoci suka yi na hakura da taron ibada saboda wannan cuta.   Yace yana sane da hali  ma...
‘Yan Sanda Sun Gayyaci Sheik Sani Khalifa Zaria Bayan Ya Jagoranci Sallar Idi

‘Yan Sanda Sun Gayyaci Sheik Sani Khalifa Zaria Bayan Ya Jagoranci Sallar Idi

Tsaro
Duk da cewa Malamin ya bi umarnin da gwamnati ta bayar na cewa kowa ya yi sallah a gida, amma kasancewar Malamin yana da almajirai da iyalai da dama hakan ya sa jama'a sun samu halartar sallar duk da cewa a gidansa dake Zaria aka gudanar da sallar.   Rahotanni sun tabbatar da cewa bayan idar da sallar ne sai ga jami'an 'yan sanda sun dira gidan malamin, inda suka ce masa ana gayyatarsa zuwa ofishinsu.     Saidai wasu daga cikin wadanda suka halarci sallan sun fusata, inda suka ki yarda a tafi da Malamin daga bisani aka fitar da malamin ta barauniyar hanya domin ya je amsa gayyarar da 'yan sandan suka yi masa.     Saidai a yayin da 'yan sandan suka zo, Sheik Sani Khalifa ya tambaye su ko an turo su ne su kama shi, sai suka ba shi amsa da ...
Mun ga wata shi yasa muka yi Idi>>‘Yan Shi’a

Mun ga wata shi yasa muka yi Idi>>‘Yan Shi’a

Uncategorized
Shugaban Mabiya akidar shi’a a jihar Sakkwato Sidi Manniru ya ce sun yi Sallar Idi ne a ranar  Juma’a, 22 ga watan Mayu, domin sun ga watan shawwal bayan sun yi azumin watan Ramadan guda 29. A zantawarsa da Aminiya, shugaban mabiya Shi’an ya ce tsarin da suka bi na ganin wata shi ne wasu mutane ne da suka yarda da su suka sanar da su an ga watan. Sanarwar ta ce anga watan ne a garin Dukkuma cikin karamar hukumar Isa da garin Yabo da Illela a sanadin haka babu makawa sai su ajiye Azumi su yi Sallah.
Yau Shaikh Dahiru Bauchi ke Sallar Idi

Yau Shaikh Dahiru Bauchi ke Sallar Idi

Uncategorized
Da safiyar ranar Asabar ne ake sa ran Shahararren malamin Mususluncin nan Shaikh Dahiru Usman Bauchi zai yi Sallar Idi, sabanin ranar Lahadi Sarkin Musulmi ya ba da umarni a yi.     Hakan dai ya biyo bayan jawabin da malamin ya yi ne cewa ya samu bayanan da suka tabbatar masa an ga wata a wurare daban-daban a Najeriya ranar Juma’a. Ganin jama’a masu yawa A cewar Shaikh Dahiru Bauchi, dukkan sharuddan da ake bukata don ajiye azumi sun tabbata.     “Da ma hukuncin da aka ba mu shi ne wata yana tabbata in aka samu mutane adilai guda biyu sun ce sun ga wata kuma an tabbatar da adalancinsu, ko ko jama’a masu yawa”, inji malamin.     “Jama’a masu yawa inda take farawa daga an samu mutum biyar baligai masu hankali, to shi ke nan a...