fbpx
Friday, June 9
Shadow

Tag: IGP Muhammad Adamu

Kungiyar Lauyoyi Ta Najeriya, NBA ta Kai karar Buhari kan tsawaita wa’adin Shugaban Yan Sanda, Adamu

Kungiyar Lauyoyi Ta Najeriya, NBA ta Kai karar Buhari kan tsawaita wa’adin Shugaban Yan Sanda, Adamu

Siyasa
Kungiyar lauyoyin Najeriya ta fara shari’a a kan Shugaba Muhammadu Buhari kan karin wa’adin Mohammed Adamu da ya yi a matsayin sufeto-janar na ‘yan sanda. An ambaci sunan Buhari, Adamu da Hukumar ‘Yan Sanda a matsayin wadanda ake kara a karar da ta shigar mai lamba FHC / L / CS / 214/2021 wacce kwamitin shigar da karar NBA na jama’a ya shigar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Legas. NBA na son kotu ta yanke hukunci kan tsarin mulki na Buhari na tsawaita wa’adin Adamu a matsayin IGP na tsawon watanni uku bayan da Adamu a ranar 1 ga Fabrairu ya kai ga cika shekaru 35 a cikin aiki. Sanarwar ta ce ana bukatar hakan ne bisa ga bukatar gaggawa da kuma aiki tukuru don sake tabbatar da fifikon doka a duk lokacin da ake kara samun rashin hukunci da kuma nuna rashin gamsuwa da jami'a...
Yanda Shugaban ‘yansandan Najeriya, IGP Adamu ya bada Biliyan 2 dan a kara masa wa’adin shekara 1 amma bai samu ba>>SR

Yanda Shugaban ‘yansandan Najeriya, IGP Adamu ya bada Biliyan 2 dan a kara masa wa’adin shekara 1 amma bai samu ba>>SR

Tsaro, Uncategorized
Sahara Reporters ta yi zargin cewa shugaban 'Yansandan Najeriya,  IGP Muhammad Adamu ya biya kudi har Naira Biliyan 2 dan a tsawaita masa wa'adin shekara 1 akan mukamin nasa amma kuma bai yi nasara ba.   Majiyar tace IGP Adamu ya bibiyi masu fada aji daga cikin sarakuna sannan kuma ya baiwa na kusa da shugaban kasa, Muhammadu Buhari kudaden toshiya har Naira Biliyan 2 dan neman a kara masa wa'adin shekara 1.   Saidai daga baya bai samu hakan ba, sai wa'adin watanni 3 aka bashi, wanda sam bai ji dadin hakan ba kamar yanda majiyar ta bayyana. Hutudole ya fahimta daga Rahoton cewa, Shugaban 'Yansandan bai yi murnar karin wa'adin watanni 3 din da aka masa ba, inda ma ya kulle ofishinsa ya ki karbar masu niyyar tayashi murna.   Majiyar tace har malamai IGP ya ka...
Sufeto Janar na ‘yan sanda ya aike da karin jami’an‘ yan sanda zuwa Katsina

Sufeto Janar na ‘yan sanda ya aike da karin jami’an‘ yan sanda zuwa Katsina

Tsaro
Sufeto-janar na ‘yan sanda, Mohammed Adamu, ya kara tura wasu jami’an‘ yan sanda zuwa jihar Katsina inda wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kaiwa wata makarantar sakandare ya bar mutane da dama cikin fargaba. Jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sanda, Frank Mba, ya ce "Tura jami'an ya biyo bayan mummunan harin da wasu mutane dauke da muggan makamai suka kai makarantar Sakandaren Kimiyya ta Gwamnati, Kankara, ta Jihar Katsina a ranar 11 ga watan Disambar 2020 wanda ya sa wasu daga cikin daliban suka bace." Daga cikin karin jami’an da aka tura jihar akwai jami’an ‘yan sanda masu binciken sirri. Zasu bada tallafin bincike ga rundunar ‘yan sanda ta jihar Katsina. Mba ya kara da cewa "Har ila yau, za su yi aiki tare da sojoji da sauran jami'an tsaro a kokarin da ake yi na cet...
Shugaban ‘yansandan Najeriya ya fara binciken neman dakatarda bin ba’asin cin zalin ‘yansanda

Shugaban ‘yansandan Najeriya ya fara binciken neman dakatarda bin ba’asin cin zalin ‘yansanda

Uncategorized
Shugaban 'yansandan Najeriya,  IGP Muhammad Adamu ya fara binciken masu kula da Shari'a na hukumar kan neman kotu ta dakatar da bin ba'asin da ake na cin zalin Rundunar SARS da aka rusa.   Kakakin hukumar 'yansandan, Frank Mba ya bayyana cewa, an tuhumi me kula da bangaren shari'a na hukumar 'yansandan kuma idan an sameshi da laifi za'a hukuntashi. Yace shugaban 'yansandan na aiki Tukuru wajan ganin an tabbatar da rusa rundunar ta SARS.
Amnesty International ta yi karya, jami’an mu kwararru ne, ba su yi harbi kan Masu Zanga-zanga ba>>IGP Adamu

Amnesty International ta yi karya, jami’an mu kwararru ne, ba su yi harbi kan Masu Zanga-zanga ba>>IGP Adamu

Siyasa
Bayan rahoton na Amnesty International, cewa sojoji da jami'an 'yan sanda sunyi harbe kan masu zanga-zangar lumana a Lekki Tollgate, Sufeto Janar na' yan sanda, Mohammed Adamu, a ranar Jumma'a ya bayyana rahoton da cewa ba gaskiya ba ne, yaudara ce kuma ya saba wa duk wasu shaidun da ake da su. Kungiyar mai zaman kanta a cikin rahotonta ta zargi sojojin Najeriya da 'yan sanda da harbe-harbe da kuma kashe masu zanga-zangar #ENDSARS a Lekki Tollgate. A cikin rahoton nata, kungiyar ta kare hakkin dan adam ta sanya hujjoji na hoto da bidiyo wadanda ke alakanta jami'an 'yan sanda da sojoji daga' sansanin 'bonny'. IGP din, yayin da yake lura da cewa rundunar ta jajirce wajen ganin Gwamnatin Tarayya ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauye na rundunar da nufin inganta ayyukan bayar da agaji,...
Abin ya isa haka,Shugaban ‘yansanda yayi gargadi tare da baiwa mataimakansa Umarnin daukar matakan dawo da Doka da Oda

Abin ya isa haka,Shugaban ‘yansanda yayi gargadi tare da baiwa mataimakansa Umarnin daukar matakan dawo da Doka da Oda

Siyasa
Shugaban 'yansandan Najeriya, IGP, Muhammadu Adamu ya bayyana cewa abin da matasa ke yi da sunan zanga-zangar SARS ya isa haka.   Shugaban 'yansandan a yau, Asabar ya bada umarni ga mataimakansa na yankunan kasarnan dana jihohi da duk sauran jami'an 'yansanda su hada kai dan dakile ci gaba da take doka. Saidai yace masu gudanar da ayyukansu bisa doka kada su razana, su hada kai da 'yansandan dan aiki tare.
Gobe za’a fara horas da ‘yansandan da zasu yi aiki a runduna SWAT, IGP ya bayyana kalarsu

Gobe za’a fara horas da ‘yansandan da zasu yi aiki a runduna SWAT, IGP ya bayyana kalarsu

Uncategorized
Shugaban 'yansandan Najeriya,  IGP Muhammad Adamu ya bayyana cewa a gobe Litinin ne idan Allah ya kaimu za'a fara horas da 'yansandan da zasu yi aiki a sabuwar Rundunar SWAT.   Ya bayyana hakane ta bakin kakakin 'yansandan Najeriya,  Frank Mba inda ya kara jaddada cewa babu ko da daya daga cikin tsaffin 'yansandan SARS da za'a saka a cikin wannan Runduna. Yace zakakuran matasa ne aka dauko wanda ke da kwarewar aiki sannan ba'a taba samunsu da wani korafin take hakkin bil'adama ba a bakin aikinsu, yace kuma lafiyayyu ne wanda zasu jure atisayen da za'a basu na Rundunar.   Yace akwai kungiyoyin kasa da kasa na kare hakkin bil'adama da zasu taimaka wajan Horas da 'yansandan, yace zasu kasance suna aiki bisa doka da oda.   “the officers selected for the ...
Bidiyon mawaki, Korede Bello tsaye a gaban shugaban ‘yansanda yana gaya masa ya hana ‘yansanda harbin masu zanga-zanga

Bidiyon mawaki, Korede Bello tsaye a gaban shugaban ‘yansanda yana gaya masa ya hana ‘yansanda harbin masu zanga-zanga

Tsaro
A jiya ne dai shugaban 'yansandan Najeriya,  IGP, Muhammadu Buhari ya gana da matasan mawakan kudancin Najeriya akan zanga-zangar SARS.   Daga cikin wanda ganawarsa da shugaban 'yansandan ta fito Fili shine Davido wanda aka zargeshi da nesanta kansa da masu zanga-zangar duk da ya karyata hakan.   A yanzu kuwa bidiyin mawaki Korede Bello ne ya bayyana inda aka ganshi shima a ganawar da akayi da shugaban 'yansandan yana rokonsa cewa dan Allah ya baiwa yaransa umarnin su daina harbin masu zanga-zanga.