fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Tag: ilimi

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada damar sauran dalibai su koma ajujuwa ciki hadda na Islamiya

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada damar sauran dalibai su koma ajujuwa ciki hadda na Islamiya

Ilimi
Gwamnatin Jihar Kaduna ta bada damar sauran Dalibai su koma Ajujuwa ciki hadda makarantun Islamiya.   Sanarwar da ta fita daga gwamnatin jihar tace ajujuwan SS2, SS1 da JS2 na Sakandare duk zasu koma karatu.   Hakanan sauran Ajujuwan Firame ma zasu koma a makarantun Gwamnati da masu zaman kansu. Ciki hadda Islamiya.   Breaking Kaduna State Government has approved Monday 22nd of February, 2021 as the second phase resumption date for SS2, SS1 and JS2 in Public and Private Secondary Schools; Primary 4, 5 and 6 for Public Primary Schools and Primary 3, 2, 1   and Nursery classes for Private Primary Schools including Islamiyah Schools respectively. I
Kaso 60 na malaman makarantar Firamare a jihar Borno basu da kwarewa

Kaso 60 na malaman makarantar Firamare a jihar Borno basu da kwarewa

Siyasa
Rahotanni sun bayyana cewa kaso 60 cikin 100 na malaman makaramtar Firamare a jihar Borno basu da kwarewa.   Kwamitin da yayi bincike kan harkar Ilimi a jihar ne ya tattaro wannan bayani.   Shugaban kwamitin, Dr. Shettima Kulima ne ya bayyana haka ga gwamna Babagana Umara Zulum a yayin da suke mika masa sakamakon binciken da suka yi a jiya, Laraba.   Yace a lokacin binciken nasu sun gano matsalolin amfani da shedar kammala karatu na bogi, wanda suka yi ritaya amma sun ki daina aiki, malaman shekarun su bai kaiba dadai sauransu. “Some are working in two or three places; Biu Local Government Area is leading in the number of such workers.   “Maiduguri Metropolitan Council is leading in workers with fake certificates with about 700 of them, fo...
Gwamnatin tarayya ta kafa kwamitin da zai tabbatar da karin Albashin Malamai da ta yi

Gwamnatin tarayya ta kafa kwamitin da zai tabbatar da karin Albashin Malamai da ta yi

Siyasa
Gwamnatin tarayya, a ranar Alhamis, ta kaddamar da wani kwamiti da zai yi aiki da hanyoyin yadda za a farfado da sana’ar koyarwa.   Wannan ci gaban ya biyo bayan karin girma da sauran kyaututtukan da shugaban kasa Muhammad Buhari yayi wa malamai yayin bikin ranar Malamai ta Duniya ta 2020 a Abuja. Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu a lokacin da yake jawabi a wani taro da akayi a Abuja ya tabbatar da cewa an nada wannan kwamitin ne domin aiwatar da wannan kudurin da akayi shi domin inganta darajar koyarwa da koyo a ƙasarnan.
Jihar Kaduna zata kafa makarantu 80 domin ilimin yara mata>>Kwamishina ilimi

Jihar Kaduna zata kafa makarantu 80 domin ilimin yara mata>>Kwamishina ilimi

Siyasa
Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce a ranar Asabar ta kammala shirye-shiryen kafa sabbin makarantun sakandare 80 a matsayin wani bangare na kokarin karawa yara mata damar samun ilimi. Kwamishinan Ilimi na jihar, Dokta Shehu Makarfi ya bayyana haka yayin da yake amsa tambayoyi yayin wani taron tattaunawa na musamman na Jihar Kaduna na samar da kasafin kudaden shekarar 2021, tare da taken, "Farfado da Kasafin Kudade". Makarfi ya bayyana cewa matakin ya zama dole biyo bayan hadari da wahalar da 'yan mata ke fuskanta wadanda ke yin tafiya mai nisa don zuwa makarantu a cikin unguwannin makwabta. Ya ce gwamnati ta riga ta gano al'ummomi 80 tare da batutuwan samun damar inda makarantun za su kasance a matsayin wani bangare na kokarin gwamnati na bunkasa ilimin yara mata.
Yanzu-Yanzu:Duk da Gargadin Gwamnatin tarayya,  Jihar Adamawa tace zata bude makarantunta 12 ga watan October

Yanzu-Yanzu:Duk da Gargadin Gwamnatin tarayya, Jihar Adamawa tace zata bude makarantunta 12 ga watan October

Siyasa
Jihar Adamawa dake Arewa maso gabashin Najeriya ta sanar da cewa zata bude makarantunta nan da 12 ga watan October idan Allah ya kaimu.   Sanarwar hakan ta fitone daga sakataren yada labarai na gwamnatin jihar, Mr. HMwashi Wonosikou. Yace gwamnan bai ji dadin tsawon lokacin da aka kulle makarantu  a jihar ba saboda zuwa annobar cutar Coronavirus/COVID-19.   Amma ya bada tabbacin cewa za'a zamar da yanayi me kyau dan kokawar daliban makarantun su. Hakanan ya baiwa ma'aikatar Ilimi ta jihar umarnin zama da masu ruwa da tsaki a harkar ilimi dan fitar da tsarin da za'a bi wajan bude makarantu.   Yace kowace makaranta dolene ta tabbatar an samar da tsarin hana yaduwar cutar Coronavirus/COVID-19 ko kuma a kulleta da cin tara. Ya jawo hankulan iyaye da su b...
Ministan Ilimi ya gana da masu ruwa da tsaki a arewa maso yamma game da sake bude Makarantu

Ministan Ilimi ya gana da masu ruwa da tsaki a arewa maso yamma game da sake bude Makarantu

Kiwon Lafiya, Uncategorized
Minisatan Ilimi Chukwuemeka Nwajiuba ya bada tabbacin sake bude makarantu nan bada jimawa ba. Ministan ya bayar da tabbacin ne a Kano ranar Asabar lokacin da ya kai ziyara gidan gwamnatin jihar Kano. Ya ce za a sanar da jama'a takamaiman ranar da za a bude makarantun bayan tuntubar dukkan masu ruwa da tsaki dake ko wanne bangare. Ministan ya ce 'taron na masu ruwa da tsaki zai fara ne daga yankin Arewa maso yamma. A nasa bangaren, Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna wanda ya tarbi Ministan, ya ce tuni Kano ta shirya tsaf don sake bude makaranta.
Jihar Akwa-Ibom ma ta saka ranar 21 ga wata dan bude makarantunta

Jihar Akwa-Ibom ma ta saka ranar 21 ga wata dan bude makarantunta

Siyasa, Uncategorized
Jihar Akwa-Ibom ta saka ranar 21 ga watan Satumba a matsayin ranar da za'a bude makarantun gaba da sakandare na jihar. Hakanan ta saka ranar 28 ga watan a matsayin ranar da za'a bude makarantun Firamare da na Kimiyya da fasaha na jihar. Kwamishinan yada labarai na jihar Ini Ememobong ne ya bayyanawa manema labarai haka ranar Juma'a a Uyo.   Yace aji 6 na Firamare ne kawai zasu koma ci gaba da karatu dan shiryawa jarabawar fita sannan dolene a bi dokokin kare yaduwar cutar Coronavirus/COVID-19.
Malaman Jihar Imo: Ku biya mu bashin albashin mu ko kuma ba za mu bude makarantu ba

Malaman Jihar Imo: Ku biya mu bashin albashin mu ko kuma ba za mu bude makarantu ba

Uncategorized
Malaman makaranta a jihar Imo sun sha alwashin ba za su sake bude makarantu ba har sai an warware musu bashin albashin da suka tara. Shugaban kungiyar Malaman Makarantun (NUT) a jihar, Philip Nwansi, wanda ya zanta da manema labarai a Owerri, a ranar Alhamis, ya ce gwamnati ba ta yi komai ba wajen biyan basussukan albashin duk da ganawa da gwamnan jihar, Hope Uzodinma kan lokuta da yawa kan batun. Ya ce Gwamnan ya yi wata ganawa da kungiyar NUT a watannin baya inda ya yi alkawarin share basussukan albashin da ake bin malamai. Nwansi ya koka da cewa har zuwa makon farko na watan Satumba, ba a biya albashin malamai kimanin 2000 a jihar ba na tsawon watanni bakwai. Ya ce “A karamar hukumar Ngor Okpala, babu wani malamin firamare da ya karbi albashi tun a watan ...
Yanzu-Yanzu: Jihar Kebbi ma na shirin yin fatali da gargadin gwamnati dan bude makarantu a 21 ga wannan watan

Yanzu-Yanzu: Jihar Kebbi ma na shirin yin fatali da gargadin gwamnati dan bude makarantu a 21 ga wannan watan

Siyasa
Gwamnatin jihar Kebbi na shirin bin sahun jihohin Legas, Kogi, da Osun wajan bide makarantun jiharta a wannan watan.   Gwamnatin jihar tuni ta fara rabon kayan kariya irinsu takunkumin rufe baki da hanci da kuma abin wanke hannu da sauransu zuwa makarantu 2008 dake fadin jihar. Kwamishinan Ilimi na matakin Farko da Firamare da Sakandare, Alhaji Muhammad Magawata Aleiro ne ya bayyana haka a wajan rabon kayayyakin. Yace suna bada shawarar a bude makarantun nan da ranar 21 ga watannan na Satumba amma shawarace a duba aga idan ta yi.   Ya kuma godewa gwamnan jihar, Atiku Bagudu bisa goyon bayan da yake baiwa bangaren Ilimi a jihar.