fbpx
Friday, June 9
Shadow

Tag: ISWAP

Tarzoma ta barke tsakanin ‘yan Boko Haram suna ta kashe junansu

Tarzoma ta barke tsakanin ‘yan Boko Haram suna ta kashe junansu

Tsaro
Mayaƙan ISWAP da na Boko Haram ɓangaren Abubakar Shekau sun yi mummunan artabu da juna kan iko da wani yanki a Tafkin Chadi. Jaridar PRNigeria ta ce ƴan ta’adda aƙalla 54 aka kashe cikin wata ɗaya a artabu tsakanin mayaƙan ISWAP da na Boko Haram ƴan ƙabilar Buduma a Jamhuriyyar Nijar. A cewar jaridar ƴan Boko Haram daga ƙabilar Buduma suka fara kai wa ISWAP harin ba-zata a ƙauyen Chikka da ISWAP ke iko da shi a ranar 3 ga watan Maris domin kwasar ganima. “Mayaƙan daga ɓangaren Shekau sun mamaye ƙauyen inda suka kashe ƴan ISWAP da dama tare da sace matansu guda biyar. Kuma mayaƙan sun saci kayayyakin abinci kafin su gudu a cikin dare.” Daga baya kuma ISWAP ta kai harin ramuwar gayya inda suka yi ɓarin wuta da ƴan Boko Haram a yankin Kaduna Ruwa da Kaiga kuma an yi hasarar rayuka...
Dan Boko Haram ya dirkawa babban Kwamandan kungiyar da wasu da dama harsashi suka mutu bisa kuskure

Dan Boko Haram ya dirkawa babban Kwamandan kungiyar da wasu da dama harsashi suka mutu bisa kuskure

Tsaro
Wani dan Boko Haram bangaren kungiyar ISWAP da ya kware a wajan iya harbi ya kashe babban kwamanda a kungiyar da wasu 4 bisa kuskure.   An kashe kwamandan me suna Ba'ana Okocha a wani wajan kungiyar ISWAP din dake da matukar hadari me suna Arinna Sorro.   Wajan ne ISWAP ke ajiye makamanta da kuma mayakanta dake zuwa daga kasashen waje dan taimaka mata da yaki.   Maharbin ya kuskure Ba'ana da mayakan Abubakar Shekau da basu shiri da ISWAP inda kuma nan take ya bude musu wuta. Eonsintelligence ta ruwaito cewa Ba'ana ne ya jagoranci kai harin Marte da kungiyar ta kwace garin gaba daya.   Saidai daga baya, Sojojin Najeriya sun kwato Marte bayan gumurzu da aka sha sosai.  Ana ci gaba da samun baraka a tsakanin Kungiyar Boko Haram data ISWAP. Th...
Boko Haram sun sace dubban Mutanen da suka koma gidajensu daga sansanin gudin Hijira

Boko Haram sun sace dubban Mutanen da suka koma gidajensu daga sansanin gudin Hijira

Tsaro
Rahotanni daga garin Kukawa na jihar Borno na cewa mayakan Kungiyar ISWAP data balle daga kungiyar Boko Haram sun dirarwa garin da yammacin jiya, Talata.   Lamarin ya farune jim kadan bayan da mutanen garin da suka shafe shekaru 2 a sansanin gudun hira suka koma garuruwansu. Hutudole ya tattaro muku daga rahoton kamfanin dillancin labaran AFP yanda wani shugaban 'yan Vigilante, Babakura Kolo ya tabbatar da faruwar lamarin. Zuwa yandai babu wata sanarwa daga hukumar soji kan harin.