fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Tag: kaduna

Gwamna El-Rufai ya fallasa daga inda ‘yan Boko Haram ke samun kudi

Gwamna El-Rufai ya fallasa daga inda ‘yan Boko Haram ke samun kudi

Laifuka, Siyasa
Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, Boko Haram na samun kudi daga wajan garkuwa da kutane da harkokin 'yan Bindiga da ake yi a Arewane.   Ya bayyana haka a hirar da aka yi dashi a Channels Tv inda kuma yace 'yan Bindigar sun mayar da hankali kan jihar Kaduna ne saboda cewar da yayi ba zai yi Sulhu dasu ba.   Gwamnan ya kuma tabbatar da matsayarsa ta kin yin Sulhu da 'yan Bindigar indaa yace kisa ne ya dace dasu.
Gwamna El-Rufai ya Musanta nada wakilai dan sulhu da ‘yan Bindiga

Gwamna El-Rufai ya Musanta nada wakilai dan sulhu da ‘yan Bindiga

Tsaro
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya musanta cewa ya nada wakilai dan yin sulhu da 'yan Bindiga.   Kwamishinan tsaron cikin gida, Samuel Aruwan ne ya bayyana haka a wata Sanarwa da ya fitar Ranar lahadi.   Yace hankalinsu ya kai kan Rahoton dake cewa gwamnatin jihar ta nada wakilai dan yin sulhu da 'yan Bindiga amma yana son ya bayyana cewa ba gaskiya bane.   Yace matsayin su na nan ba zasu yi sulhu da 'yan Bindigar ba kuma maganar gaskiya itace duk wanda aka kama za'a yi masa hukunci daidai dashi. Kaduna,said on Sunday, that the attention of the Kaduna State Government under the leadership of Governor Nasir El-Rufai has been drawn to reports in the media that it has appointed representatives to interface with bandits on its behalf. ...
Yan Bindiga Sun Kashe Tsohon Kansila Tare da Wani Mutum a Kaduna

Yan Bindiga Sun Kashe Tsohon Kansila Tare da Wani Mutum a Kaduna

Tsaro
Wasu ‘yan bindiga sun kashe Dayyabu Jafar, wani tsohon kansila yayin da yake aiki a gonarsa da ke Ungwan Fada na Unguwar Gayam da ke karamar Hukumar Birnin Gwari a Jihar Kaduna. 'Yan bindigar sun kuma kai wa wani mutum mai suna Yusuf Dallatu hari a Kasuwan Magani da ke karamar hukumar Kajuru a wani harin na daban. Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Gidaje, Samuel Aruwan, wanda ya tabbatar da kisan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya ce hukumomin tsaro ne suka sanar da abin da ya faru. Aruwan ya ce sojojin a karkashin inuwar Operation Safe Haven (OPSH) sun bayar da rahoton wani hari da wasu gungun makiyaya suka kaiwa wasu makiyaya da shanunsu a kan hanyar Shanun Mabushi a yankin Zangon Kataf da ke jihar. A cewarsa, makiyayan, wadanda suke aiki a...
Yadda wata mata taita aman jini bayan anyi mata allurar COVID-19 a Kaduna

Yadda wata mata taita aman jini bayan anyi mata allurar COVID-19 a Kaduna

Kiwon Lafiya
Wata ma’aikaciyar gwamnati a Babban Asibitin Gwamna Awan a jihar Kaduna, Misis Hannatu Tanko ta bayyana cewa ta yi amai da jini bayan ta karbi allurar rigakafin ta COVID-19. Misis Tanko ta ce ta sha allurar ne a ranar 25 ga Maris din 2021 kuma daga baya ta ji jiri. Ta bayyana cewa a ranar asabar 28 ga Maris ta fara aman jini sai aka garzaya da ita asibiti. Tanko a wani bidiyo mai dauke da hoto ta ce anyi mata allurar ne a sakatariyar Kaduna ta Kudu saboda an fada musu cewa idan basuyi ba, ba za a biya su albashi ba. “Ina ta yin amai da jini ta hanci da baki. An kai ni asibitin Gwamna Awan, inda aka ba ni magunguna don rage ciwo. ”Sun yi min allura don rage min ciwon kai sannan suka ce in zo a gwada ni. Ni kuma an ce in sayi panadol. Na bar asibitin ne sabod...
Yan bindiga sun kai hari a Kaduna, inda suka kashe mutane takwas, tare da jikkata hudu a Kajuru, Giwa da Chikun

Yan bindiga sun kai hari a Kaduna, inda suka kashe mutane takwas, tare da jikkata hudu a Kajuru, Giwa da Chikun

Tsaro
Gwamnatin jihar Kaduna a ranar Laraba ta ce mutane takwas sun mutu, yayin da wasu hudu suka samu munanan raunuka yayin harin da ‘yan bindiga suka kai a kananan hukumomin Giwa, Kajuru da Chikun na jihar Kaduna. Mista Samuel Aruwan, kwamishanan tsaron cikin gida da harkokin cikin gida na jihar Kaduna ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Laraba. A cewar Aruwan, "Mutane takwas ne suka mutu, sannan hudu suka ji rauni sakamakon wasu 'yan bindiga da suka kai hare-hare da aka kai kan kananan hukumomin Chikun, Giwa da Kajuru." "Wadannan an zayyana su ne a cikin rahotannin da hukumomin tsaro suka gabatarwa gwamnatin jihar Kaduna." “A Kan Hawa Zankoro, kusa da Ungwan Yako a karamar hukumar Chikun, wasu‘ yan bindiga dauke da bindiga sun harbi wata mota, daga nan sai ta wunts...
Gwamnan Kaduna ya cire dansa daga makarantar Gwamnati yayin da satar dalibai ke ci gaba da kazanta

Gwamnan Kaduna ya cire dansa daga makarantar Gwamnati yayin da satar dalibai ke ci gaba da kazanta

Siyasa
Rahotanni daga jihar Kaduna na cewa, Gwamnan Jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya cire dansa daga makarantar Gwamnati ta Capital school da ya sakashi a baya.   El-Rufai a shekarar 2019, ya cika alkawarin da yayi inda ya kai dansa, Abubakar makarantar ya fara karatu da 'ya'yan Alakawa.   Saidai bayan ziyarar da Sahara Reporters ta kai makarantar, ta samu Labarin tunda aka koma Makaranta dan gwamnan bai koma ba.   Ta kuma samu cewa hakan ba ya rasa Nasaba da matsalar tsaro.
Tankokin dakon man fetur 11 sun kone a wani gareji da gobara ta tashi a Kaduna

Tankokin dakon man fetur 11 sun kone a wani gareji da gobara ta tashi a Kaduna

Uncategorized
Motocin dakon man fetur 11 sun kone a ranar Talata lokacin da gobara ta kama wani garejin ajiye motoci a Anguwan Mu’azu a Kaduna. Babban Sakataren Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Kaduna (KADSEMA), Abdulahi Hassan, ya tabbatar da faruwar lamarin. Shugaban KADSEMA, wanda ya je wurin domin tantance yadda barnar ta kasance, ya ce lamarin gobarar ya haifar da gano wasu ayyukan bata gari da suka hada da kayayyakin mai a yankin. Ya ce hukumar za ta binciki sa hannun mazauna garin da kuma mambobin kungiyar a cikin irin wadannan ayyukan da ake zargin sun haifar da tashin gobarar. Shaidun gani da ido sun sanar cewa wasu mutane kalilan sun samu raunuka kuma an garzaya da su asibiti don kulawa.
Mijina ya gayamin cewa ko ni aka sace ba zai biya kudin fansa ba>>Matar Gwamnan Kaduna

Mijina ya gayamin cewa ko ni aka sace ba zai biya kudin fansa ba>>Matar Gwamnan Kaduna

Tsaro
Matar Gwamnan jihar Kaduna, Hadiza Isma'il El-Rufai ta bayyana cewa, mijin nata ya gaya mata idan aka sace ta ba zai biya kufin fansa ba.   Ta bayyana hakane ta shafinta na sada zumunta a yayin da ta kai ziyara gonarta.   Jihar Kaduna dai na fama da matsalar masu garkuwa da mutane. Wanda sukan nemi a biya kudin fansa masu yawa kamin su saki wanda suka kama. “At my farm today. Anyone thinking of ** me should not bother. The man has already warned me that he will not pay any ******,” she tweeted, preferring to have the words ‘kidnapping’ and ‘ransom’ in asterisks.
Kamfanin giya na Kaduna shine yafi kowane kamfani biyan haraji me yawa a Jihar

Kamfanin giya na Kaduna shine yafi kowane kamfani biyan haraji me yawa a Jihar

Kasuwanci
Kamfanin Dake yin giya na Kaduna, Naigerian Breweries ya samu lambar yabo ta ma'aikatar tattara haraji ta jihar a matsayin kamfanin da yafi kowane bayar da kudin haraji.   Shugaban hukumar,  Zaid Abubakar ya bayyana jinjina ga kamfanin inda yayi kira ga sauran kamfanoni dake jihar da masu biyan harajo su yi koyi dashi.   Yace daga shekarar 2018 zuwa 2020, kamfanin giyar ya biya jihar Kaduna kudin haraji da suka kai Biliyan 1.4. “The essence of the award was to motivate taxpayers in the state to continue to pay their taxes voluntarily so that the state government will continue to deliver quality services to the people,” he explained.
Yan sanda sun ceto mutum 5, sun kashe ɗan fashi a Kaduna

Yan sanda sun ceto mutum 5, sun kashe ɗan fashi a Kaduna

Tsaro
Jami'an tsaro a Jihar Kaduna sun yi nasarar ceto mutum biyar da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a yankin Birnin Gwari. Kwamishinan Tsaro na jihar, Samuel Aruwan, ya ce lamarin ya faru ne da tsakar ranar Juma'a bayan dakaru sun samu rahoton cewa wasu 'yan bindiga sun tare hanyar Birnin Gewari zuwa Kaduna. A cewar kwamishinan, nan take jami'an tsaro suka isa kuma suka yi nasarar tserar da mutanen bayan fafatwa da 'yan fashin. A wata fafatawar ta daban, jami'an sun kashe ɗan fashi ɗaya tare da kama wani bayan sun buɗe wa motar 'yan sanda wuta. Aruwan ya ce bincike ya nuna cewa mutanen suna ɗauke ne da makamai domin kai wa 'yan fashin daji a Zamfara da Katsina da Kaduna da Neja. Kazalika, rundunar jami'an tsaron haɗin gwiwa ta yi nasarar ƙwato shanu 32 da tumakai 10, waɗanda ...