fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Tag: Katsina covid19

Gwamnatin jihar Katsina tasha al’washin samar da cibiyoyin killace masu cutar coronavirus a fadin jihar

Gwamnatin jihar Katsina tasha al’washin samar da cibiyoyin killace masu cutar coronavirus a fadin jihar

Kiwon Lafiya
Gwamnatin jihar Katsina ta ce tana gina cibiyoyin keɓewa, tare da yunkurin samar da gadaje guda  722, a duk faɗin jihar don inganta kula da marassa lafiyar dake fama da cutar COVID-19. Gwamna Aminu Masari ya sanar da haka lokacin da ya amshi motocin daukar marasa lafiya guda uku, wanda gidauniyar BUA ta bayar a jihar, ranar Alhamis a cikin garin Katsina. A cewar sa “Mu da kanmu muna gina cibiyoyin keɓewa a wurare daban-daban a fadin jihar, tare da yunkurin samar da gadajan kwanciya guda 722, don kula da marasa lafiya dake fama da cutar Coronavirus.   Haka zalika gwamnan ya bayyana cewa an gama gina cibiyar killacewa guda daya a jihar.   Shima dai A ta bakin Shugaban Gidauniyar na BUA, Alhaji Abdussamad Ishaq Rabiu, ya ce an ba da motocin guda uku don inganta har...
Hotuna: BUA ya baiwa jihar Katsina tallafin Motocin daukar Mara lafiya 3

Hotuna: BUA ya baiwa jihar Katsina tallafin Motocin daukar Mara lafiya 3

Siyasa
Gidauniyar me kamfanin BUA, Abdulsamad Rabiu watau BUA Foundation ta baiwa jihar Katsina tallafin motocin daukar mara lafiya 3.   BUA ya bada tallafin motocinne dan ci gaba da yaki da cutar Coronavirus/COVID-19 a jihar. Gwamnan jihar Katsina,  Aminu Bello Masari ne ya bayyana haka ta shafinsa na Twitter, kamar yanda hutudole ya samo.   Ya yabawa BUA da wannan kokari inda yace Allah ya saka masa da Alheri.   Saidai yayi amfani da wannan dama inda ya roki BUA din ya tallafa musu a kan ginin gurin killace masu cutar Coronavirus/COVID-19 da jihar ke yi me daukar gadaje 700. https://twitter.com/GovernorMasari/status/1266005983618314240?s=19 A baya dai BUA ya bayar da tallafi me kwari sosai dan tallafawa yaki da cutar Coronavirus/COVID-19 a m...
“Zamu binciki menene musabbabin yawan mace macan da ake samu a jihar Katsina – Gwamna Aminu Masari

“Zamu binciki menene musabbabin yawan mace macan da ake samu a jihar Katsina – Gwamna Aminu Masari

Kiwon Lafiya
Gwamnatin jihar Katsina ta ce tana binciken musabbabin aukuwar yawan mace mace da ke faruwa wanda ba a saba gani ba a kullum a fadin jihar.   Gwamna Aminu Masari ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Talata a lokacin da yake gabatar da bayani kan cutar COVID-19 a cikin jihar.   Ya ce gwamnati ta horar da likitocin da za su yi bincike kan abin da ke haddasa mace-macen a jihar, wanda mafi yawan wanda suka mutu a jihar tsofaffi ne.   Gwamnan Masari ya tabbatar da cewa "Masu binciken cutar za su samo samfuran wasu daga cikin mutanen da suka mutu don tabbatar da gano ko cutar coronavirus ce tai ajalinsu ko kuma ba ita bace. in ji shi. Gwamnan ya ce yanzu haka gwamnatin jihar tana da samfurori kusan 400 wadanda ke jiran gwaji daga Cibiyar dak...
Jihar katsina ta sallami mutum 6 bayan da suka warke daga cutar corona

Jihar katsina ta sallami mutum 6 bayan da suka warke daga cutar corona

Kiwon Lafiya
An sallami mutum shida cikin goma sha hudu da aka killace a asibitin kwararru na Gwamnatin Tarayya da ke Katsina, sakamakon kula da su na tsawon kwana goma sha tara da suka kwashe a asibitin ana kula da su.   Shugaban Asibitin Kwararru ta Tarayya da ke jihar Katsina, Dr. Bello Sulaiman Muhammad ne ya tabbatar wa manema labarai a gidan Gwamnatin jihar Katsina.   Dr. Bello Sulaiman ya cigaba da cewa ” a cikin wadanda suka warke kuma har an sallame su akwai yaro dan shekara biyu da rabi, sauran biyar din wadanda suka warke garas din daga Daura suke.   Sauran takwas din kuma ana cigaba da kula da lafiyarsu kuma suna samun sauki sosai. Kuma nan gaba kadan zaa gwada su.