
Likitoci na shirin shiga yajin aiki a Najeriya
Ƙungiyar likitoci ta ƙasa ta buƙaci mambobinta su shirya shiga yajin aikin gama gari daga ranar 31 ga watan Maris din 2021.
Jaridar The Punch ta rawaito cewa wannan shi ne karo na uku da likitocin ke shiga yajin aiki a cikin watanni 9 a ƙasar.
Ƙungiyar ita ce mafi girma cikin ƙungiyoyin ma'aikata lafiya, kuma mambobinta su suka kasance kan gaba wajen yaƙi da annobar korona.
Ko a watan Yuni da Satumba 2021 sai da suka shiga irin wannan yajin saboda matsalolin albashi da alawus-alawus da rashin walwala a fanin aiki.