fbpx
Thursday, June 8
Shadow

Tag: Mali

Tsohon shugaban kasar Mali, Amadou Toumani Toure ya rasu

Tsohon shugaban kasar Mali, Amadou Toumani Toure ya rasu

Siyasa
Tsohon Shugaban Mali Amadou Toumani Touré ya rasu yana da shekara 72. Ya mutu ne da safiyar yau Talata a Turkiyya, inda likitoci ke kula da shi bayan ya isa birnin Istambul a 'yan kwanaki da suka gabata. Kafin ya bar Mali, an yi masa tiyatar gaggawa a zuciya a wani asibiti da ke babban birnin ƙasar, Bamako. Ya shugabanci Mali daga 2002 har zuwa sanda aka tumɓuke shi a juyin mulkin sojoji a 2012, wanda Janar Amadou Haya Sanogo ya jagoranta. An yabi Mista Touré game da kawo ƙarshen mulkin sojoji na tsawon shekaru tare da miƙa shi ga farar hula ta hanyar shirya zaɓe a 1992. Ana yi masa laƙabi da "sojan dimokuraɗiyya". Mali's former president, Amadou Toumani Touré, has died at the age of 72, a family member and a doctor said on Tuesday November 10.   "Amadou Toumani Toure di...
An bai wa sojojin Mali mako ɗaya su naɗa shugaban farar hula

An bai wa sojojin Mali mako ɗaya su naɗa shugaban farar hula

Uncategorized
An bai wa sojojin da suka hamɓarar da mulki a Mali mako guda kacal zuwa 15 ga watan Satumba su naɗa sabon shugaban farar hula a ƙasar. Shugabannin ƙasashen yammacin Afrika na Ecowas ne suka yanke wannan hukunci suna cewa naɗin zai buɗe hanyar yin sabbin zaɓuka a ƙasar. Har yanzu sojojin ba su mayar da martani kan sanarwar da aka yi a ranar Litinin ɗin ba, wadda aka yi a taron da shugabannin ƙasashe takwas na yammacin Afrikan suka halarta a Nijar. Ƙungiyar Ecowas na son miƙa mulkin ya kasance cikin shekara ɗaya, amma a baya sojojin sun ce suna buƙatar isasshen lokaci na kamar a ƙalla shekara biyu. Sojojin juyin mulkin sun yi ta taruka da shugabannin siyasa. A ranar Lahadi ne aka tafi da hamɓararren shugaban Malin Ibrahim Boubacar Keïta ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa don kai...
An garzaya da hambararren shugaban kasar Mali UAE dan Neman Lafiya

An garzaya da hambararren shugaban kasar Mali UAE dan Neman Lafiya

Siyasa, Uncategorized
Rahotanni daga kasar Mali na cewa an garzaya da tsohon shugaban kasar da Sojoji suka hambarar a juyin Mulki, Ibrahim Boubacar Keita zuwa kasar UAE dan neman Lafiya.   Keita ya samu rakiyar Matarsa, Amina sa wasu likitoci da jami'an tsro. Kamfanin dillancin labaran AP ya bayyana cewa da yammavin Yau, Asabar ne aka tafi da tsohon shugaban zuwa UAE. A baya dai mun ji cewa an garzaya da tsohon shugaban kasar Asibiti a Mali bayan da ciwon mutuwar barin jiki ta kamashi.   A wani Labari me dangantaka da wannan kuma Rahotanni daga kasar na cewa sojojin masar 2 ne aka kashe a wani hari.
Kuma Dai: An kashe sojojin Mali 10 a harin Kwantan Bauna

Kuma Dai: An kashe sojojin Mali 10 a harin Kwantan Bauna

Tsaro
Rahotanni daga kasar Mali na cewa sojojin kasar 10 ne suka rasa rayukansu a iyakar kasar da Mauritania.   Yankin ya dade yana fama da hare-haren 'yan tada kayar baya wanda kuma ana zargin sune suka yi kisan. Wata Majiya daga yankin da lamarin ya faru tace sojojin suma sun kashe 'yan Bindigar 20 saidai an lalata musu kusan motoci2. Mun kasa bacci, gidajen mu sun rika motsi saboda fashewar abubuwa, wani mazaunin yankin ya gayawa kamfanin dillancin labaran AFP.
An kwantar da tsohon shugaban Mali Keita a asibiti

An kwantar da tsohon shugaban Mali Keita a asibiti

Siyasa
Rahotanni daga Mali na cewa an kwantar da hambararren shugaban kasar a asibiti. Kamfanin dillacin labarai na Associated Press ya ambato majiyoyi biyu daga asibiti na cewa tsohon shugaban kasar yana samun kulawa. An hambarar da Ibrahim Boubakar Keita mai shekara 75 daga kan mulki ne makonni biyu da suka wuce sannan kuma aka tsare shi na tsawon kwana goma a wani sansanin soji kafin a ba shi damar walwala. Lokacin da ake gudanar da tattaunawar sulhu, Mr Keita ya ce ba ya son komawa kan mulki. 'Yan hamayya sun kwashe watanni suna kira a gare shi ya sauka daga mulki, inda suka dora alhakin tabarbarewar tattalin arziki da tsaro, da kuma cin hanci da rashawa a kansa.
Sojojin Kasar Mali Sun Jinkirta Taron Tattauna Mika Mulki Ga Fararan Hula

Sojojin Kasar Mali Sun Jinkirta Taron Tattauna Mika Mulki Ga Fararan Hula

Siyasa
Shugabannin sojan Mali sun fada a ranar Asabar cewa, za su jinkirta taronsu na farko kan batun mika mulki saboda “dalilai na Gudanarwa”, kusan makwanni biyu bayan hambarar da shugaban a cikin juyin mulki. Sojojin sun gayyaci kungiyoyin fararen hula, kungiyoyin siyasa da tsoffin 'yan tawaye don tattaunawa a ranar Asabar, amma sun ce a cikin wata sanarwa cewa an dage ganawar zuwa wani lokaci nan gaba. Hadin gwiwar kungiyoyin zanga-zangar adawa wadanda suka yi adawa da tsohon shugaban kasar, Ibrahim Boubacar Keita, kungiyar Yuli 5, ba a gayyace su shiga cikin taron ba. Kungiyar ta bukaci rundunar sojin kasar da ta ba ta dama wajen mika mulki zuwa ga farar hula da sojoji suka yi alkawarin, duk da cewa ba'a yi wani tsarin hakan ba.
ECOWAS ta baiwa sojojin Mali shekara 1 su mika mulki ga farar hula, Shugaba Buhari ya goyi bayan haka

ECOWAS ta baiwa sojojin Mali shekara 1 su mika mulki ga farar hula, Shugaba Buhari ya goyi bayan haka

Siyasa
Kungiyar kasashen yammacin Africa ta ECOWAS ta baiwa sojojin kasar Mali watanni 12 su gaggauta Mika mulki ga farar Hula.   Kungiyar ta cimma wanan matsaya ne bayan ganawar da ta yi da membobinta a yau. Da yake magana a wajan taron, Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana goyon bayansa ga wannan mataki. Kakakin shugaban kasar, Femi Adesina ya bayyana cewa shugaba Buhari ya nuna jin dadinsa kan yanda aka saki tsohon shugaban kasar Malin da aka hambarar da gwamnatinsa, Ibrahim Boubacar Keita inda kuma yayi kira da a saki sauran shuwagabannin siyasar da ake rike dasu a kasar.   Shugaban ya bayyana cewa wakilan kungiyar ECOWAS da suka je kasar Mali basu cimma wata Matsaya ba amma yana baiwa Sojojin shawarar su yadda da mika mulki cikin shekara 1 idan suna neman h...
Shugaban kasar Mali da akawa Juyin Mulki ya shaki Iskar ‘yanci

Shugaban kasar Mali da akawa Juyin Mulki ya shaki Iskar ‘yanci

Siyasa
Rahotanni daga kasar Mali na cewa, Shugaban kasar da akawa juyin Mulki, Ibrahim Boubacar Keita ya shaki Iskar 'yanci a yau bayan da sojojin da suke rike dashi suka sallameshi.   Me magana da yawun sojojin da suka yi juyin Mulkin, Djibilla Maiga ne ya tabbatar da haka inda yace tsohon shugaban kasar har ya koma gidansa. Saidai daga haka bai bayar da wani cikakken bayani ba, kamar yanda Reuters ta bayyana.