A makon daya gabata ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya zabi tsohon gwamnan, Borno Shettima a matsayin abokin takararsa.
Wanda hakan ya jawo cece kuce a kasar musamman ta wurin mabiya addinin Kirista domin sunce wannan ba adalci bane kuma ba zasu yi APC ba.
Sannan tikitin Musulmi da Musulmin na APC yasa tauraruwar Peter Obi ta fara disashewa a Arewacin kasar.
A kwanakin baya rahotanni sun bayyana cewa Peter Obi na samun daukaka sosai a Arewacin kasar nan amma yanzu APC ta disashe wannan tauraruwar tasa bayan ta tsayar da Musulmai.