fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Wasu malamai bakin ciki suke da ci gaban da gwamnatin Buhari ta kawo shiyasa suke ta magana akan matsalar tsaro>>Fadar Shugaban kasa

Kakakin shugaban kasa, Femi Adesina ya bayyana cewa magana dake tunzura mutane na daga cikin matsalar tsaron da ake fama da ita a Najeriya.

 

Femi ya bayyana hakane a shafinsa na Facebook, inda yace irin wadannan mutane masu kalaman tunzura jama’a basa magana akan manyan ayyukan da gwamnatinsu ke yi.

 

Yace irin wadannan malamai dama mutane suna son su samu wata dama ne kawai da kuma wani karfin iko shiyasa suke irin wadannan maganganu.

 

A kwanakin nan ne dai aka dakatar da limamin masallacin Apo na ‘yan majalisu dake Abuja kan maganar da yayi akan matsalar tsaro bayan harin da aka kai kan jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *