fbpx
Thursday, June 8
Shadow

Wata Sabuwa: Hankula zasu tashi idan aka ji masu hannu a harin da ‘yan Boko Haram suka kai gidan yarin Kuje>>Inji Gwamnati

Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ya bayyana cewa, an mikawa shugaban kasa, Muhammadu Buhari bincike na farko da aka yi akan harin da Boko Haram suka kai gidan yarin Kuje dake babban birnin tarayya, Abuja.

 

Yace idan aka ji wadanda ke da hannu a lamarin, hankula zasu tashi.

 

Yace kuma akwai jami’an hukumar tsaron gidan yarin da ake zargi da sakaci wajan rashin daukar marakan da suka dace sannan kuma akwai wadanda ake zargi da bada hadin kai wajan yin harin.

Karanta wannan  Bidiyo: Anga 'yansandan Najariya na cin zarafin wasu matasa

 

Yace duk wanda aka samu da hannu za’a hukuntashi.

 

Ya bayyana hakane bayan zaman majalisar tsaro ta kasa da ya wakana a yau, Alhamis a Abuja.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *