fbpx
Saturday, September 23
Shadow

Yadda wani magidanci ya babbake gidansa tare da matarsa da yaransa a ciki

Wani magidanci a yankin Lekki Phase 1 dake jihar Legas ya babbaka gida sa saboda ya samu sabani da matar sa.

wannan lamarin ya faru ne a ranar lahadi kuma shugaban hukumar hukumar dake kashe wuta, Adukunke Hassan ya tabbatar da faruwar shi.

Inda yace wani mutun ne ya sanar dasu mai suna Kola, kuma sun hanzarta zuwa gidan sun kashe wutar domin kar ta shafi sauran gidajen dake kusa dasu.

Kuma a yadda ya fahimci lamarin magidanci ya samu sabani da matarsa ne shekaru biyu da suka gabata wanda hakan yasa ya koma wani gidan nasa da zama.

Karanta wannan  Za a fara gwajin riga-kafin cutar HIV a Afirka ta Kudu

Magidancin wanda ya kasa fadin sunansa kwatsam ranar lahadi yazo da fetur ya babbaka gidan tare da matarsa da yaransa a ciki.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *