‘Yan Najeriya na ci gaba da jinjina wa Kotun Kolin Kasar saboda hukuncin da ta yanke na tilasta wa Babban Bankin Kasar, CBN na watsi da wa’adin ranar 10 ga watan nan na dakatar da amfani da tsoffin kudaden da aka sauya wadanda karancinsu ya haifar da matsaloli baki daya.