fbpx
Thursday, December 7
Shadow

Yan sanda sun kama ‘ƙwararren ɓarawon akuya’ a Kaduna

Yan sanda sun kama ‘ƙwararren ɓarawon akuya’ a Kaduna

 

Kaduna Police CommandCopyright: Kaduna Police Command

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta ce ta kama wani matashi da take zargi “ya ƙware” a satar akuyoyi a ƙaramar hukumar Kagarko da ke jihar.

 

Kakakin rundunar, ASP Mansur Hassan, ya faɗa wa kamfanin labarai na Najeriya NAN cewa sun kama mutumin ne a ranar Asabar a ƙauyen Pasali Konu.

 

A cewarsa, matashin mai shekara 20 ɗan asalin ƙauyen Igwa ne kuma an kama shi “ɗauke da makamai masu haɗari da kuma takunkumi a fuskarsa”.

Karanta wannan  Na rantse da Allah da Rugar Fulani aka kai harin bom ba kan masu Maulidi ba da hotuna za'a watsa ace an yi nasara akan 'yan ta'adda>>inji Sheikh Asadussunah Kaduna

 

“Wanda ake zargin ya amsa laifinsa cewa su biyu ne suka je ƙuyen don satar akuyoyi,” a cewar ASP Hassan.

 

Ya ƙara da cewa wanda suke tare da matashin da ake zargin ya tsere bayan ya hangi dakarun ‘yan sanda, amma suna ci gaba da neman sa.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *