fbpx
Saturday, March 25
Shadow

‘Yan Shi’a na Zanga-Zanga a Abuja inda suke neman a baiwa Zakzaky Fasfonsa

Kungiyar ‘yan Shi’a ta nemi hukumar kare hakkin bil’adama ta kasa data saka baki wajan yiwa gwamnatin tarayya magana a sakarwa Zakzaky takardunsa na Fasfon tafiye-tafiye dana matarsa.

 

Sun yi Zanga-Zanga a ofishin hukumar kare hakkin bil’adama dake Abuja inda suka zargi gwamnatin tarayya da take hakkin Zakzaky.

 

Kungiyar tace watanni 9 kenan da sakin Zakzaky da kuma wankeshi daga zarge-zargen da ake masa da kotu tayi.

 

Amma hukumomin Najeriya sun ki bashi Fasfsonsa dan yaje neman magani da iyalansa a kasar waje.

Karanta wannan  An Ce Wasu Masu Gine-Gine Dake Kewaye Da Masallacin Idin Kano Sun Soma Saka Su A Kasuwa Biyo Bayan Faduwar Gwamnati, Inda Jama'a Ke Gudun Saye Don Kada Su Yi Gwari

 

Wakilin kungiyar ya gayawa manema labarai cewa, sun jira amma gwamnati bata dauki matakin da ya dace ba shiyasa suka dawo yin Zanga-Zanga.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *